Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-06-15@16:04:21 GMT

‘Yan Sanda Sun Mika Bakin Haure 165  A Birnin Kebbi

Published: 6th, February 2025 GMT

‘Yan Sanda Sun Mika Bakin Haure 165  A Birnin Kebbi

Rundunar ‘yan sandan jihar Kebbi, ta kama wasu bakin haure 165 da aka ce sun fito ne daga kasashen da ke amfani da harshen Faransanci tare da mika su ga hukumar kula da shige da fice ta kasa dake jihar domin gudanar da bincike.

 

A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, SP Nafiu Abubakar ya fitar kuma ya mika wa gidan rediyon Najeriya a jihar Kebbi, ya ce, bisa rahoton bayanan sirri, an gano sama da mutum dari biyu a wani gida mai dakuna uku da ke unguwar Kuwait a cikin birnin Birnin Kebbi.

 

Sanarwar ta ce, tawagar jami’an ‘yan sanda da ke sashin binciken manyan laifuka (SCID) ne suka kai samame unguwar inda suka yi nasarar cafke mutane dari da sittin da biyar (165).

 

Ya bayyana cewa, yayin da ake gudanar da bincike, an gano cewa, dukkan wadanda ake zargin sun fito ne daga kasashen da Faransa ta yiwa mulkin mallaka da suka hada da Burkina Faso, Jamhuriyar Benin, Jamhuriyar Nijar, Mali da Ivory Coast.

 

A cewar sanarwar, bincike ya kara nuna cewa, wadanda ake zargin suna zaune ne a Najeriya ba tare da wasu takardu masu inganci ba kuma ana zarginsu da hannu a cikin shirin Qnet Ponzi.

 

Sanarwar ta ce, bayan kammala binciken farko da rundunar ta gudanar, an mika wadanda ake zargin bakin haure zuwa hukumar shige da fice ta kasa reshen jihar Kebbi, domin ci gaba da bincike da kuma daukar matakin da ya dace.

 

PR/ Abdullahi Tukur

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Miliyoyin Mutane Sun Gudanar  Da Bukukuwan “Idin Gadir” A Tehran Da Sauran Garuruwan Iran

A yau Asabar aka gudanar da bikin ranar ” Idin Gadir” a nan birnin Tehran, wanda ya tashi daga dandalin “Inqilab” zuwa dandalin ” Azadi” mai nisan kilo mita 10. Bisa la’akari da halin yake da ake ciki, an bai wa bikin na bana taken: Iran ce, takobin Zulfikar Na Imam Ali.”

Miliyoyin mutane ne dai su ka cika filin bikin na birnin Tehran da mutane su ka fara taruwa tun da tsakar rana, har zuwa bayan faduwar rana. A bisa kirdado kusan  mutane miliyan 3 ne su ka taru a nan Tehran.

A cikin sauran birane da garuruwan Iran an yi wannan irin gangamin na raya ranar Idin Gadir wanda yake tattare da girmama shahidan da su ka kwanta dama sanadiyyar hare-haren ta’addancin HKI. Haka nan kuma mahalarta bikin na Gadir sun jinjinawa dakarun kare juyin musulunci na Iran da kuma sojojin kasar akan martanin da su ka mayarwa da HKI a daren jiya Juma’a da kuma a yau Asabar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Harin Benuwe: ’Yan sanda sun tarwatsa masu zanga-zanga
  • Trump ya dakatar da kamen baƙin haure a wasu wurare na Amurka
  • An Yi Zanga-zangar Nuna Goyon Baya Ga Kin Amincewa Da Bakin Haure A Amurka 
  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Miliyoyin Mutane Sun Gudanar  Da Bukukuwan “Idin Gadir” A Tehran Da Sauran Garuruwan Iran
  • Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • Hajjin 2025: Yadda Alhazan Nijeriya 7 Suka Rasa Rayukansu A Saudi Arabiya
  • Mutum ɗaya ya tsira da ransa cikin 242 a hatsarin jirgin India