Turkiya Tana Shirin Karbar Sansanin Sojan Da Faransa Ta Fice Daga Cikinsa A Kasar Chadi
Published: 5th, February 2025 GMT
Rahotanni sun ambaci cewa bayan ficewar sojan Faransa na karshe daga sansanin Abaci dake gabacin kasar Chadi,kasar Turkiya tana shirin maye gurbinta.
Wata majiyar kasar Turkiya ta shaidawa wata kafar labaru ta Afirka cewa, Ankara tana shirin girke jiragen yaki marasa matuki a cikin sansanin dake kan iyaka da kasar Libya akokarin da take yi na cike gurbin da Faransa ta bari, da zummar tabbatar da kanta a cikin wanann yankin na Afirka.
Gwamnatin Chadi ta bai wa Turkiya sansanin na Abaci a karkashin yarjejeniyar da kasashen biyu su ka cimmawa a tsakiyar watan da ya gabata,bayan doguwar tattaunawa da aka yi a tsakanin jami’an gwmanatocin kasashen biyu.
Haka nan kuma rahoton ya ce, kasar Turkiya ta bai wa gwamnatin kasar ta Chadi jiragen sama marasa matuki samfurin Beyraghdar. Haka nan kuma da akwai masu bayar da shawara na soja da dama daga kasar ta Turkiya a cikin kasar ta Chadi.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
NAF Na Shirin Siyo Jiragen Yaki Masu Saukar Ungulu Daga Amurka
Ya ce, “Muna matukar godiya ga gwamnatin Amurka saboda dorewar kawancen dabarun hadin gwiwa da Nijeriya.”
Ya kara da cewa, sayan jirage masu saukar ungulu na AH-1Z Viper zai kara inganta yakin da NAF ke yi, da kwazon aiki.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp