Aminiya:
2025-05-29@19:01:13 GMT

Tinubu zai tafi Faransa daga nan ya zarce Habasha

Published: 5th, February 2025 GMT

Shugaba Bola Tinubu a wannan Larabar zai bar Nijeriya zuwa ƙasar Faransa domin kai wata ziyara ta ƙashin kai.

Daga nan kuma Shugaba Tinubu zai wuce ƙasar Habasha inda zai halarci taron gamayyar ƙungiyar ƙasashen Afirka ta AU.

NAHCON ta tsawaita wa’adin biyan kuɗin Hajjin bana Dalilin da farashin citta ya yi tashin gwauron zabo

Mai bai wa Tinubu shawara kan yaɗa labarai, Bayo Onanuga a shafinsa na X, ya ce Tinubu zai tafi Paris ɗin ne gabanin tafiyar da zai yi zuwa Addis Ababa, babban birnin Habasha domin taron ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU).

A lokacin taron da za a yi a birnin na Addis Ababa a farkon mako mai zuwa, Shugaba Tinubu zai gana da shugabannin ƙasashen Afirka domin taron ƙungiyar da za a gudanar daga ranar 12 zuwa 16 ga watan Fabrairun 2025.

A yayin ziyararsa a Faransa, Tinubu zai gana da takwaran aikinsa na Faransa Emmanuel Macron.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Faransa

এছাড়াও পড়ুন:

OPEC+ Ta Fara Shirin Ayyana Yawan Man Fetur Da Zata Haka Zuwa Sekara Ta 2027

Kungiyar kasashe masu arzikin man fetur da kuma kawayenta a wajen kungiyar sun gudanar da taro a birnin Riyad na kasar Saudia inda suka tattauna kan yawan man fetur da zasu haka daga shekara da ta 2027.

Shafin yada labarai na tanar gizo na kasar Saudia Arab News ya bayyana cewa wannan yana daga cikin abinda kasashe suka amince a bayan kuma a halin yanzu kungiyar ta rika ta tsara yawan man da ko wace kasa zata haka daga shekara ta 2022 har zuwa shekara ta 2026.

Labarin ya kara da cewa kungiyar tana da tsare tsaren haka man fetur har guda uku biyu suna tafiya kamar yadda suka tsara a yayinda daya kuma sun warewa kasashe 8 daga cikinsu su aiwatar da shi. Wannan tsarin yana daga cikin tsare tsaren kungiyar na dogon zango.

A halin yanzu dai farshin man yana kan $60 a cikin watan Afrilun da ya gabata, Sannan shi ne farashi mafi karanci tun shekaru 4 da suka gabata, kuma sana diyyar kara kudaden fiton da Trump yayi farashin ya tashi zuwa $65 kan ko wace ganga.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ɗalibai Sun Rubuta Jarrabawar WAEC Cikin Dare A Duhu
  • OPEC+ Ta Fara Shirin Ayyana Yawan Man Fetur Da Zata Haka Zuwa Sekara Ta 2027
  • Buhari Ya Yabi Tinubu, Ya Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Rage Tsammani Da Dogon Buri
  • Majalisar Nasarawa Ta Bukaci A Cire Malamai 1000 Daga Aikin Tantancewar Da Ake Yiwa Malamai
  • NEJERIYA A YAU: Sai Yaushe ’Yan Najeriya Za Su Ci Gajiyar Manufofin Shugaba Tinubu?
  • Tinubu ya ɗaga darajar Kwalejin Kimiyya  ta Kabo Zuwa Jami’ar Fasaha ta Tarayya
  • Tinubu na neman ciyo bashin Naira tiriliyan 39 daga kasashen waje
  • Sojojin Sudan Sun Fatattaki Dakarun Kai Daukin Gaggawa Daga Sansaninsu Da Ke Birnin Omdurman
  • Shugaba Tinubu Ya Amince Da Ɗaga Likafar Kwalejin Fasaha Ta Kabo Zuwa Jami’a
  • Shugaba Tinubu Ya Amince Da Sauya Kabo Polytechnic Zuwa Jami’ar Kimiyya Da Fasaha Kabo