Tinubu zai tafi Faransa daga nan ya zarce Habasha
Published: 5th, February 2025 GMT
Shugaba Bola Tinubu a wannan Larabar zai bar Nijeriya zuwa ƙasar Faransa domin kai wata ziyara ta ƙashin kai.
Daga nan kuma Shugaba Tinubu zai wuce ƙasar Habasha inda zai halarci taron gamayyar ƙungiyar ƙasashen Afirka ta AU.
NAHCON ta tsawaita wa’adin biyan kuɗin Hajjin bana Dalilin da farashin citta ya yi tashin gwauron zaboMai bai wa Tinubu shawara kan yaɗa labarai, Bayo Onanuga a shafinsa na X, ya ce Tinubu zai tafi Paris ɗin ne gabanin tafiyar da zai yi zuwa Addis Ababa, babban birnin Habasha domin taron ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU).
A lokacin taron da za a yi a birnin na Addis Ababa a farkon mako mai zuwa, Shugaba Tinubu zai gana da shugabannin ƙasashen Afirka domin taron ƙungiyar da za a gudanar daga ranar 12 zuwa 16 ga watan Fabrairun 2025.
A yayin ziyararsa a Faransa, Tinubu zai gana da takwaran aikinsa na Faransa Emmanuel Macron.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Faransa
এছাড়াও পড়ুন:
IMF na Shirin aikewa da wata tawaga zuwa Senegal domin tattauna batun basussukan kaaar
Asusun ba da lamuni na duniya IMF ya fada a wannan alhamis cewa yana shirin aikewa da tawaga zuwa kasar Senegal a cikin watan Augusta domin tattauna yadda aza magance matsalar basussukan da ke kan kasar da kuma fara tattaunawa kan tsarin sabon shirin lamuni.
Kasar Senegal na fama da bashin biliyoyin daloli da gwamnatin da ta shude ta karba, lamarin da ya sanya asusun lamuni na duniya IMF ya dakatar da shirin ba da lamuni ga kasar.
A nasa bangaren kuma, wani mai magana da yawun IMF ya ce, “Asusun na bukatar karin bayanai kafin ya karfafa kimanta halin da ake ciki na basussukan kasar Senegal, sannan yana bukatar yarjejeniya kan muhimman matakan gyara.”
Ya kara da cewa, “Da zarar mun cimma matsaya kan manyan matakan gyara, hukumar ta IMF za ta sake yin nazari kan batun, yana mai bayyana cewa “zai yiwu a cimma matsaya kan wadannan matakan nan da makonni masu zuwa.”
Kakakin ya kara da cewa “Hukumar lamuni ta duniya IMF ta yi kiyasi bisa ga sabbin bayanai daga hukumomin kasar Senegal cewa basusukan da aka boye wanda gwamnatin da ta gabata ta karb, sun kai dala biliyan 11.3 a karshen shekarar 2023. Wannan ya hada da wani kaso na bashin kamfanonin gwamnati da aka kiyasta kusan kashi 7.4% na GDP.”
Kakakin IMF ya ce zai ba da bayanai ga hukumar kan yadda lamarin ya faru , yana mai cewa “IMF na gudanar da bincike na cikin gida da tantancewa a matsayin wani bangare na rashin bayar da rahotonni da suka dace.”