Jami’ar ABU da ke Zariya ta yi sabon shugaba
Published: 5th, February 2025 GMT
Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya ta sanar da naɗa sabon shugabanta, Farfesa Adamu Ahmed.
Majalisar Gudanarwar jami’ar ce ta zaɓi Farfesa Adamu Ahmed a matsayin wanda zai maye gurbin Farfesa Kabir Bala.
An soma rigimar haraji tsakanin China da Amurka Dalilin da farashin citta ya yi tashin gwauron zaboAn sanar da zaɓen Farfesa Adamu da misalin ƙarfe 6:15 na safiyar wannan Larabar a yayin zaman Majalisar Gudanarwar jami’ar wanda Mahmud Yayale Ahmed CFR ya jagoranta.
Farfesa Adamu Ahmed dai malami ne a sashen nazarin tsara birane na jami’ar ta ABU.
Ya taɓa riƙe muƙamin Darektan Cibiyar Bunƙasa Jami’ar kuma a yanzu shi ne Uban Jami’ar Ilimi ta Tarayya da ke Kano.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Farfesa Adamu Ahmed Jami ar ABU Farfesa Adamu
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Majalisar Ƙoli ta Shari’ar Musulunci a Najeriya ya rasu
Allah Ya yi wa Shugaban Majalisar Ƙoli ta Shari’ar Muslunci a Najeriya, Sheikh Abdul Rasheed Hadiyatullah, rasuwa.
Babban Mufti na ƙasar Yarbawa, Sheikh Daood Imran Molaasan, ne ya sanar da rasuwar Sheikh Abdul Rasheed Hadiyatullah a cikin wata sanarwa da ya sanya hannu a kai a daren Litinin.
Sai dai bai bayar da cikakken bayani game da inda Sheikh Hadiyatullah ya rasu ko kuma lokacin da hakan ya faru ba.
Sheikh Molaasan ya bayyana cewa rasuwar marigayi Sheikh Hadiyatullah ta bar giɓi mai wuyar cikewa a shugabancin Musulunci na ƙasar.
Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin Najeriya“An haife shi a garin Iwo a Jihar Osun kuma an san shi da dabi’u Musulunci. Sheikh Hadiyatullah ya kasance fitaccen malamin Musulunci kuma masanin shari’a, wanda an san shi da ƙoƙarinsa na neman a aiwatar da Shari’a Musulunci a tsarin mulkin Najeriya, tattaunawa tsakanin addinai, da zaman lafiya a tsakanin al’ummomin Najeriya masu bambancin addini.
“Ya yi aiki a matsayin Shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci na tsawon shekaru, inda ya jagorance ta a lokutan ƙalubalen zamantakewa da ci gaba.
“Sheikh Hadiyatullah ya fara karatun addinin Musulunci a wurin malaman gida kafin ya ci gaba da karatunsa a ƙasashen waje.
“Ya samu girmamawa a faɗin Najeriya da ma wajenta saboda zurfin ilminsa a fannin fiƙihun Musulunci da kuma salon shugabancinsa mai nutsuwa da tsayin daka kan akida,” kamar yadda Molaasan ya bayyana.
Ya kuma yi addu’ar Allah ya gafarta wa Sheikh Hadiyatullah ya kuma ba shi Aljannatul Firdaus.