Aminiya:
2025-09-17@23:34:54 GMT

Dalilin da farashin citta ya yi tashin gwauron zabo

Published: 5th, February 2025 GMT

A yayin da farashin buhu daya na danyar citta da ke a matsayin iri ya yi tashin gwauron zabon da ba a taɓa ganin irin sa ba, inda ake sayar da shi a kan Naira 210,000 kowane buhu, shi kuwa busasshen buhun citta ana sayar da shi ne daga Naira dubu 500,000 zuwa Naira 550,000 a yankin Kudancin Jihar Kaduna da aka fi noman ta a Nijeriya.

Hakan ba ya rasa nasaba da matsalar kwayoyin cutar da suka lahanta mafi yawan cittar da aka noma a 2024, wanda ya yi sanadiyyar karancin irin cittan da kuma hauhawar farashin taki da magunguna da sauran ayyukan noman cittar.

Hausawa sun yi bikin cika shekara 153 da zama a garin Owerri DAGA LARABA: Yadda Al’adun Aure A Ƙasar Hausa Suka Koma ‘Event Centre’

A 2024, manoman citta a Kudancin Kaduna, inda daya daga cikin inda ake samar da mafi ingancin citta a duniya suka gamu da mummunan ibtila’in da ya lalata musu citta, inda wata kwayar cutar fungus ta halaka mafi yawan amfanin gonakinsu, wanda ya haifar da asarar biliyoyin Naira.

Manoman da suka dogara kacokan a kan noman citta a matsayin babban hanyar samun kudin shiga, sun shiga cikin halin zulumi da ya kai ga yawancinsu sun bar gonakinsu ba tare da noman citta ba, yayin da da dama daga cikinsu suka koma noman shinkafa da wake da gero da kurkur da dankalin Turawa da kuma masara don rage asarar da suka yi.

Michael John, wani manomin citta daga garin Kushe Kowi da ke Karamar Hukumar Kagarko, ya bayyana halin da ya shiga a lokacin bullar cutar.

Ya ce, “kafin wannan cutar, nakan noma buhu 350 na citta kowace shekara. Amma tun bayan bullar cutar, na daina noman citta gaba daya.

Cutar ta lalata jarina, kuma ba ni da kudin da zan sake farawa. Farashin irin citta a yanzu ya sa ba zan iya komawa noman ba.”

Ya bayyana cewa, shekaru da dama da suka gabata, al’ummarsu kan noma doya ce da gyada.

“Amma daga baya sun mayar da hankali a kan noman citta kawai. Sai dai wannan matakin da suka dauka ya haifar musu da matsalar karyewar tattalin arziki.

“Mun rasa jarinmu, yanzu kuma muna fama da talauci,” in ji shi.

Ya kara da cewa, bai taba samun wani tallafi daga gwamnati ko rancen kudi don tallafa wa harkar noman citta ba, inda ya yi kira ga gwamnati da ta taimaka wa manoman karkara irinsa, ganin yadda farashin Irin da na taki da magungunan kwari da na sufuri ke kara tsananta.

Illar cutar ta fungus da tsadar

Irin sun haifar da raguwar cittan da ake samarwa daga Kudancin Kaduna.

Wasu ’yan kasuwar citta a garin Kafanchan da ke Karamar Hukumar Jama’a sun bayyana halin da ake ciki a sanadiyyar rashin isasshiyar cittar a yankin.

“A baya, daga watan Nuwamba zuwa Janairu, muna iya jigilar motocin tirela sama da 200 na citta kowane mako daga Kudancin Kaduna,” in ji Babangida Abubakar, wani mai harkar citta a Kafanchan.

“A bana, sai da ƙyar muke iya fita da tireloli biyu a mako. Wannan saboda yadda manoma da yawa ba su samu damar noman cittar ba ne sosai,’’ in ji shi Rebecca Yakubu, wata ‘yar kasuwa, ta bayyana kaduwarta game da karancin cittar, ta ce, “karancin citta ya sa farashinta ya yi tsada sosai.’’

“Kodayake ga wadanda ke da cittar da za su sayar, suna samun amfani sosai, amma idan manoma suka ci gaba da barin noman citta, za mu iya fuskantar rugujewar kasuwar citta a Kudancin Kaduna baki daya.”

Kira ga Gwamnati

Yusuf Danjuma, wani masanin aikin gona a Kudancin Kaduna, ya yi kira ga gwamnati da ta shiga lamarin don magance wannan matsalar.

Ya ba da shawarar kafa gonakin gwaji don samar da iri mai inganci da za a rarraba ga manoma cikin sauki.

“Dole ne mu nemi mafita a kai,” in ji Danjuma.

“Ya kamata gwamnati ta kafa gonakin gwaji a cikin al’ummomin da ke noman cittar.

“Wannan zai sake dawo da amincin ga manoma da karfafa su komawa ga noman citta.”

Ya kuma jaddada muhimmancin horar da manoma kan gano da kuma magance cututtuka domin guje wa sake faruwar lamarin nan gaba.

Gudunmawar kungiyoyi da taimakekeniya

Haka kuma, manoma da dama sun yi kira ga kungiyoyi masu zaman kansu da gwamnatoci da su samar da iri mai rahusa tare da tallafa musu da rance mai saukin biya don ci gaba da noman.

Wannan zai rage tsadar sake fara noman da ya zama babban cikas ga yawancin manoman.

Yayin da ake fuskantar wannan matsalar, hanya guda da za a iya bi don ceto harkar noman citta a Kudancin Kaduna ita ce hadin kai da hadakar duk masu ruwa da tsaki, wanda zai taimaka wajen dawo da martabar yankin a matsayin babbar cibiyar noma da samar da citta mai inganci.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: ga gwamnati

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu

Sojoji biyu sun ji rauni bayan wani harin kwanton baya da ’yan bindiga suka kai kan ayarin motocin Kwamandan kwamandan Rundunar Sojoji ta 382 Ƙaramar Hukumar Faskari ta jihar Katsina.

Lamarin ya faru ne a ƙauyen Ruwan Godiya, kan hanyar Sheme–Kankara, lokacin da tawagar Operation Fansan Yamma (OPFY) ke wucewa.

Ganau sun ce sojojin na kan hanyar ziyartar sansanonin sojoji a yankunan Faskari da Mabai da Ɗan Ali lokacin da aka kai musu hari.

Sai dai sun yi nasarar tunkarar ’yan bindigar har suka kuvuta, kodayake sojoji biyu sun samu raunuka na harbi kuma aka kai su asibitin sojoji domin jinya.

An kai wa sojojin harin ne a rana ɗaya da shugabannin al’ummar Faskari suka zauna da wakilan ’yan bindiga domin rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya.

’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara Hauhawar farashi ya ragu a watan Agusta — NBS

Hakan ya sanya Faskari zama ƙaramar hukuma ta baya-bayan nan da ta shiga irin wannan sulhu bayan ƙananan hukumomin Ɗanmusa da Jibia, Batsari da Ƙanƙara, Kurfi da Musawa.

Yarjejeniyar na neman kawo ƙarshen tashin-tashina, garkuwa da mutane da kuma ƙaura da ake fama da su a jihar.

Amma akwai shakku kan ɗorewar ta, domin wasu daga cikin shugabannin ’yan bindigar sun bayyana cewa sulhun ya shafi ƙananan hukumomin da suka shiga yarjejeniyar kawai, lamarin da ya janyo tsoron cewa sauran wuraren da ba su rattaba hannu ba, suna iya ci gaba da fuskantar hare-hare.

Wasu mazauna Ruwan Godiya sun ce ayyukan ’yan bindiga na ƙara ta’azzara a sassan Katsina duk da yarjejeniyar sulhun da aka ƙulla da wasu daga cikin shugabanninsu.

Masana sun bayyana cewa hakan ya nuna raunin irin waɗannan tsare-tsare na sulhu, tare da tabbatar da buƙatar ƙarin sa-ido a yankunan da ke fuskantar barazana.

Sulhun Faskari da ’yan bindiga

Ƙaramar Hukumar Faskari ta zama ta baya-bayan nan a Jihar Katsina da ta shiga yarjejeniyar zaman lafiya da ’yan bindiga, domin kawo ƙarshen kashe-kashe, garkuwa da mutane da kuma ƙaura da ake fama da su a yankin.

Kamar sauran sulhunan da aka kulla a ƙananan hukumomi guda shida, sharuddan yarjejeniyar sun ba wa ’yan bindiga damar shiga garuruwa da kasuwanni da asibitoci.

Haka kuma, za su sako duk wanda aka yi garkuwa da shi ba tare da sharaɗin ba. A sakamakon haka, al’umma za su iya komawa gona da kasuwanni cikin kwanciyar hankali ba tare da fargabar farmaki ba.

Yarjejeniyar ta biyo bayan taron al’umma da aka yi a Faskari, inda fitaccen shugaban ’yan bindiga, Ado Aliero, wanda ake nema ruwa a jallo, ya tabbatar wa manoma tsaronsu.

“Daga yau kowa ya koma gona cikin kwanciyar hankali; ba abin da zai faru a Faskari baki ɗaya,” in ji Aliero cikin wani bidiyo da Aminiya ta gani.

Aliero ya ɗora laifin rushewar yarjejeniyar da aka yi a baya kan cafke ɗansa, yana mai cewa ya bi duk hanyoyin lumana, amma abin ya gagara, kafin ya koma tayar da hankali.

A wani bidiyo daban kuma, wani ɗan bindiga da aka gani sanye da rigar harsashi ya zargi hukumomi da nuna wariya da rashin adalci, yana mai cewa sulhu na gaskiya zai tabbata ne kawai idan aka yi adalci ga kowa.

Sai dai duk da rahotannin da ke cewa jami’an gwamnati da na tsaro sun halarci taron, gwamnatin Jihar Katsina ta nesanta kanta daga wannan yarjejeniyar.

Akwai masu kawo cikas — Gwamna Raɗɗa

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Raɗɗa, ya ce duk da irin ƙalubalen tsaro da ake fuskanta, gwamnatinsa na samun ci-gaba, sai dai akwai masu ƙoƙarin kawo cikas.
Ya bayyana haka ne a wani taron shawarwari da aka gudanar a Katsina ranar Lahadi, wanda ya tattaro manyan masu ruwa da tsaki ciki har da sarakunan gargajiya da shugabannin siyasa da shugabannin tsaro da masana, ’yan kasuwa da shugabannin addini.
Gwamnan ya ce tsaro ne ginshiƙin ajandar ci-gabansa tare da ilimi da noma da kiwon lafiya da kuma tallafa wa ƙanana da matsakaitan ’yan kasuwa.
Ya sanar da cewa gwamnati za ta gina gidaje 152 ga iyalan da aka raba da muhallansu a Jibia, tare da shirya shirin tallafa wa tubabbun ’yan ta’adda da suka domin kada su koma ɓarna.
Haka kuma ya yaba wa jami’an sa-kai da ƙungiyoyin tsaro na gari da suka taimaka wajen dawo da ƙwarin gwiwa a tsakanin jama’a.
Cikin manyan da suka halarci taron akwai tsohon Gwamna Aminu Bello Masari da dattijo Sanata Abu Ibrahim da fitaccen dan kasuwa Alhaji Ɗahiru Mangal da Sarkin Daura Alhaji Faruk Umar Faruk da tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama, Hadi Sirika, Ministan Gidaje Arc. Ahmed Ɗangiwa, da kuma Hadiza Bala Usman mai ba shugaban ƙasa shawara kan tsare-tsare.
Sauran sun hada da tsohon Daraktan DSS Alhaji Lawal Daura, tsohon Daraktan NIA Ambasada Ahmed Rufai, tsohon Shugaban Kamfanin na NNPC Injiniya Abubakar Yar’adua da Babban Alƙalin jihar Alhaji Musa Ɗanladi, da kuma manyan hafsoshin soja da dama da suka yi ritaya.
Hakazalika, an samu halartar manyan jami’ai, malamai daga jami’o’i da ƙungiyoyin ƙwadago da ƙungiyoyin farar hula da ’yan kasuwa da sauran shugabanni daga sassa daban-daban na jihar.
Gwamna Radda ya jaddada cewa zai ci gaba da karɓar suka da shawarwari daga masu kishin ƙasa, tare da kira ga haɗin kai domin shawo kan matsalolin tsaro da tattalin arziki da jihar ke fama da su.

Abin da mahalarta suka ce

A nasa vangarenm Mataimakin Gwamnan Jihar Katsina, Faruk Lawal Joɓe, ya bayyana cewa gwamnatin Raɗɗa ta samar da sama da ayyuka 35,903 a fannoni daban-daban ta karkashin manufar “Gina Makomarka.”

Joɓe ya bayyana ce an samar da ayyukan ne ta hanyar ɗaukar malamai da shugabannin unguwanni da jami’an tsaro na sa da mafarauta da sauransu domin su riƙa taka rawa wajen wanzar da zaman lafiya.

Ya kuma yi ƙarin haske kan aikin Sabunta Birane na Katsina State Urban Renewal da ya lashe Naira biliyan 74.9 wanda ya shafi manyan ayyuka a Daura da Funtua da Katsina.

Ayyukan sun haɗa da gina sabuwar hanyar Eastern Bypass mai tsawon kilomita 24, titi mai hannu biyu a cikin Katsina, gyaran tituna a Daura da Funtua, da kuma kammala wasu muhimman hanyoyin karkara.

A nasa jawabin, Kwamishinan Tsaro na Cikin Gida, Dakta Nasir Muazu, ya ce gwamnatin Raɗɗa ta ɗauki matakin rashin tattaunawa da ’yan bindiga.

Ya ce abubuwan da ke haifar da ta’addanci sun haɗa da son zuciya da rikice-rikicen albarkatu da sauyin yanayi, da kuma rashin adalci a cikin al’umma.

Ya ƙara da cewa daga 2011 zuwa 2015 matsalar ta tsaya a ƙananan hukumomi biyar, amma ta bazu zuwa 25 a lokacin tsohon Gwamna Aminu Masari bayan shirin afuwa ya faskara.

Kwamishinan ya bayyana cewa hare-haren soji sun lalata maɓoyar ’yan bindiga da dama, sun buɗe manyan hanyoyi, sannan mutum 628 da suka tsira daga hare-hare sun samu kulawar lafiya a bana.

Ya ce yanzu dakarun Community Watch, masu aikin sa-kai da ’yan banga suna mara baya ga jami’an tsaro da ke amfani da jirage marasa matuƙa da makamai da motocin aiki.

Shugaban Ƙungiyar ƙwadago (TUC) na jihar, Muntari Abdu Ruma, ya gargaɗi gwamnati ta yi taka-tsantsan da yarjejeniyar zaman lafiya da ’yan bindiga lura da yarjejeniyar Kankara ta 2016 da ta gagara.

Haka kuma, shugaban ƙungiyoyin farar hula na jihar, Malam Abdulrahman Abdullahi, ya ce akwai buƙatar ƙarin haɗin kai tsakanin jihohin Arewa maso Yamma wajen yaki da ’yan bindiga. Ya yi nuni da cewa ziyarar da dattawan Katsina suka kai wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu a bisa jagorancin Gwamna Raɗɗa ta fara haifar da sakamako mai kyau a Ƙanƙara da Faskari, amma dole a ci gaba da ayyuka cikin tsari.

A nasa ɓangaren, Sanata Ibrahim Tsauri na jam’iyyar adawa PDP, ya ce taron ya fi karkata wajen bayyana nasarorin gwamnati fiye da ba wa mahalarta dama su yi sharhi.

Duk da haka ya ce idan aka ci gaba da irin waɗannan taruka, za su iya kawo sauyi ga jihar bayan shekaru 15 na ƙalubale.

An ce mahalarta taron sun yi alkawarin mara wa gwamnati baya wajen shawo kan matsalar samari, musamman shaye-shaye da sauran laifuka.

Sauran muhimman shawarwarin sun haɗa da haɗe hanyoyin sadarwa a wuri guda da nufin samun nasarar wannan abu da aka sanya a gaba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • NECO ta saki sakamakon jarabawar 2025
  • NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
  • DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya
  • Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • ’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • Hauhawar farashi ya ragu a watan Agusta — NBS
  • Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin