Shugaban Majalisar Wakilai Dr Abbas Tajuddeen, ya bayyana kaduwarsa bisa rasuwar fitaccen dan kasuwa kuma mai taimakon jama’a, Alhaji Bala Abdulwahab da ke Zariya, wanda aka fi sani da Albabello.

A wata sanarwa da mai ba shi shawara na musamman kan harkokin yada labarai Malam Musa Abdullahi Krishi ya fitar, Dakta Abbas Tajuddeen, ya ce masarautar Zazzau da jihar Kaduna sun yi rashin babban dan kasuwa wanda ya sadaukar da rayuwarsa gaba daya wajen yi wa al’umma hidima.

Shugaban majalisar ya jaddada cewa, Albabello, ta hanyar sahihancinsa na kasuwanci, ya samar da ayyukan yi ga dubban jama’a a Zariya da ma fadin kasar nan, ta hanyar amfani da rassan kamfaninsa daban-daban.

Ya ci gaba da cewa Albabello, ya kuma gina makarantun firamare da sakandare da dama don inganta ilimi;  da masallatai, domin ci gaban al’umma.

Hakazalika, a yayin rayuwarsa marigayin ya  dauki nauyin bayar da tallafin karatu ga dalibai don yin karatu a Najeriya da kasashen waje, da sauransu.

Dr Tajuddeen, ya yi addu’a ga  Allah SWT dayYa ji kan marigayi Alhaji Bala Abdulwahab, Ya kuma bai wa iyalansa hakurin jure rashin.

Alhaji Bala Abdulwahab, wanda shi ne wanda ya assasa kamfanin Albabello Trading Company Limited da ke Zariya, ya rasu ne a ranar Litinin 3 ga watan Fabrairun 2025, yana da shekaru 68.

Daga Salihu Tsibiri

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Rasuwa Shugaban Majalisar Wakilai

এছাড়াও পড়ুন:

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi

Hukumar NDLEA ta bayyana cewa wata ƙungiyar masu safarar miyagun ƙwayoyi ce a filin jirgin sama na Kano ta boye jakunkunan ƙwayoyi a cikin kayan matafiyan.

An kama shugaban ƙungiyar, Ali Abubakar Mohammed (wanda aka fi sani da Bello Karama), tare da wasu abokan aikinsa.

Hukumar ta ce mutanen ukun ba su da laifi kuma an zalunce su ne kawai.

An saki su ne bayan bincike da kuma ƙoƙarin diflomasiyya na tsawon makonni.

Lamarin ya tayar da hankali kan tsaro a filayen jirgin sama a Nijeriya da yadda masu aikata laifuka ke amfani da fasinjoji marasa laifi.

Hukumar ta ce za a ɗauki ƙarin matakai don hana faruwar irin wannan lamari.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kammala Ziyarar Yini 3 A Ma’aikatar Kananan Hukumomin Jihar
  • Microsoft ya ƙwace shafukan wasu kamfanoni 340 a Najeriya
  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • Karamar Hukumar Birnin Kano Ta Kaddamar Da Kula Da Lafiyar Ido Kyauta
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • Mutuwar majinyata: Asibitin Aminu Kano na roƙon KEDCO ya dawo da wutar lantarki
  • Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)