Kasashen EU3 Sun Ce, Dauke Takunkuman Tattalin Arzikin Wa Kasar Iran Ya Fi Karfinsu
Published: 3rd, February 2025 GMT
Shuwagabannin kasashen turai guda uku wato EU3 sun bayyana cewa daukewa Iran takunkuman tattalin arzikin da aka dorawa kasar ya fi karfinsu.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto shugaban hukumar makamashin nukliya na kasar Iran yana fadar haka a wata hira ta musamman da ta hada ta da tashar.
Mohammad Eslami ya ce kasashen turan guda uku wadanda suka hada da Jamus, Faransa da Ingila sun aiko masa da sako inda suke tabbatar haka. A cikin shugaban Muhammad Eslami ya fadawa tashar talabijan ta Presstv irin ci gaban masu yawa wadanda JMI ta samu a cikin shekarun da suka gabata.
Shugaban ya kara da cewa sakon da EU3 ya nuna irin yadda rikicin shirin Nukliyar kasar Iran ta ke da sarkakiya. Ya kuma kara da cewa hukumar makamashin nukliya ta duniya ce yakamata ta kare hakkin duk wata ka a duniya kan hakkin mallakan fasahar nukliyan ta zaman lafiya.
Shugaban hukumar makamashin nukliya ya bayyana cewa, har yanzun yarjeniyar JCPOA tana raye, amma iran zata maida hankali a kanta ne kawai idan dayan bangaren ya dawo kan ta.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kasar Faransa Ta Yi Allah Wadai Da Harin Ta’addancin Da Aka Kai Birnin Zahedan Na Kasar Iran
Gwamnatin kasar Faransa ta yi kakkausar suka tare da tofin Allah tsine kan harin ta’addancin da aka kai birnin Zahidan na kasar Iran
Ma’aikatar harkokin wajen Faransa ta yi Allah-wadai da kakkausar murya kan harin ta’addancin birnin Zahidan na kasar Iran, tare da jaddada adawar kasarta kan duk wani harin ta’addanci da aka kai kan fararen hula.
Ma’aikatar harkokin wajen Faransa ta fitar da wata sanarwa inda ta ce, birnin Paris na matukar yin Allah wadai da harin ta’addanci da aka kai a birnin Zahidan na kasar Iran a ranar 26 ga watan Yuli, wanda ya yi sanadin mutuwar fararen hula da dama ciki har da uwa da kuma ‘yarta.
Sanarwar ta kara da cewa, “A yayin da take mika ta’aziyyarmu ga iyalan wadanda suka mutu, suna fatan samun sauki cikin gaggawa ga wadanda suka jikkata a wannan harin ta’addanci.”
Wani abin lura a nan shi ne cewa, a safiyar ranar Asabar 26 ga watan Yuli ne wasu ‘yan ta’adda suka kai hari kan ginin hukumar shari’a ta cibiyar birnin Zahidan, fadar mulkin lardin Sistan da Baluchestan a kudu maso gabashin kasar Iran, inda suka kashe da kuma jikkata wasu Iraniyawa.