Jagoran kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen, Sayyid Abdulmalik al-Husi ya  yaba wa yadda kungiyar Hamas ta jajurce da ci gaba da wanzuwa a dunkunle duk da cewa kwamandan dakarunta Muhamamd Dhaif ya yi shahada.

Jagoran kungiyar ta Ansarullah ya gabatar da jawabi ne na tunawa da zagayowar lokacin shahadar Salih al-Simad wanda daya ne daga cikin manyan shugabannin Ansarullah, ya kara da cewa, ci gaba da wanzuwar kungiyar ta Hamas yana daga cikin muhimman ayyukan da Muhammad Dhaif ya aiwatar a lokacin rayuwarsa.

Sayyid Abdulmalik al-Husi ya mika sakon ta’aziyyar shahadar Muhammad Dhaif ga kungiyar ta Hamas, tare da bayyana shi a matsayin daya daga cikin manyan jagorori abin koyi saboda ruhinsa na imani mai karfi, azama da ruhi na jihadi.

Da yake Magana akan yadda al’ummar Yemen su ka taimakawa gwgawarmayar Falasadinawa,  Sayyid Abdulmalik al-Husi, ya kara da cewa; Idan har ‘yan sahayoniya su ka koma yaki, to su ma mutanen Yemen za su koma fagen dagar taimakawa Falasdinawa.

Dangane da kasar Lebanon ma Sayyid Abdulmalik al-Husi ya yi yabo akan yadda al’ummar kudancin kasar suka koma garuruwansu da hakan yake a matsayin babban jihadi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

HOTUNA: Yadda aka dawo da ’yan Najeriya 203 daga Libya

Kalli yadda aka karɓi ’yan Najeriya guda 203 da aka dawo da su daga ƙasar Libya.

(Hoto: Onyekachukwu Obi).

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tarayyar Afirka ta dage takunkumin da ta kakabawa Gabon
  • Katafaren Jirgin Daukar Jiragen Yaki Na Kasar Amurka Harry Truman Zai Fice Daga Tekun Maliya
  • HOTUNA: Yadda aka dawo da ’yan Najeriya 203 daga Libya
  • HKI Tana Amfani Yunwa A Matsayin Makamin Yaki  A Kan Falasdinawa A Gaza
  • Shugaban Kungiyar Hizbullah Ya Abbaci Abubuwa 3 Wadanda Yakamata Kasar Ta Maida Hankali A Kansu
  • Shugaban Putin Na Rasha Ya Bada Sanarwan Tsagaita Wuta Da Ukraine Na Sa’o’ii 72
  • Ɗaukewar wutar lantarki ta tsayar da al’amura a Sifaniya da Portugal
  • Gwamnatin Tarayya Ta Umurci WAEC, NECO Su Koma Amfani Da CBT Nan Da 2026
  • Rasha ta ayyana tsagaita wuta ita kaɗai a yakinta da Ukraine
  • Jiragen Yakin Amurka Sun Kashe Mutane Da Dama A lardin Sa’ada Na Kasar Yemen