’Yan bindiga sun kashe mutum 3 sun sace 24 a Zamfara
Published: 31st, January 2025 GMT
’Yan bindiga sun kashe mutane uku tare da yin garkuwa da wasu 24 a wasu jerin hare-hare a wasu kauyuka hudu a Ƙaramar Hukumar Shinkafi da ke Jihar Zamfara.
’Yan ta’adan sun kai hare-haren ne ranar Alhamis, a ƙauyukan Shinkafi da Jangeru da Shanawa da Birnin Yero.
A garin Shinkafi, ’yan bindigar sun kashe mutum uku tare da yin garkuwa da wasu tara, ciki har da mata hudu.
Mazauna garin sun bayyana cewa maharan sun bude wuta kan mai uwa da wabi, lamarin da ya haifar da fargaba.
Direba cikin barasa ya murƙushe sojoji sun mutu a Legas Ya tona kabarin mijin mahaifiyarsa ya yanke kansaA kauyen Birnin Yero, ’yan bindiga sun kai hari a wani masallaci a lokacin sallar magariba, suka yi awon gaba da mutane takwas tare da raunata wasu da dama wadanda suka tsere zuwa cikin daji.
Sun kuma kai hari kauyen Shanawa, inda suka sace mutane hudu. Wannan harin ya faru ne kwana guda bayan an sako wasu mazauna kauyen guda 12 bayan an biya kudin fansa naira miliyan 12.
A Jangeru, an yi garkuwa da wata mata amma daga baya aka yi watsi da ita a cikin daji bayan da ’yan bindigar sun tabbatar ba za ta iya ci gaba da tafiya ba.
Wani mazaunin garin ya bayyana cewa sun sumar da ita ne, sai daga bisani ta dawo hayyacinta ta koma kauyensu.
’Yan ta’addan sun kuma gargadi mazuna kauyukan Kwari da Kurya, inda suka bai wa mazauna kauyukan wa’adin kwanaki uku su fice daga gidajensu ko kuma su fuskanci farmaki.
Sai dai mazauna kauyen Kurya sun sha alwashin yin fito-na-fito da wannan barazana, inda suka bayyana cewa sun gaji da biyan haraji da kudin fansa.
Sun kuma yi kira ga gwamnati da ta kara yawan jami’an tsaro domin taimaka musu wajen kare kansu daga hare-hare a nan gaba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Garkuwa Zamfara
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
Dakarun Operation Haɗin Kai sun kama mut biyar da ake zargin suna taimaka wa ’yan ta’adda da kayan aiki.
Daga cikinsu har da wani ɗan ƙasar China da ya ce shi mai harkar ma’adinai ne.
Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin TarayyaAn kama su ne a lokacin kai wani samame da aka gudanar daga 5 zuwa 7 ga watan Yuni a ƙananan hukumomin Kukawa da Ngala na Jihar Borno, da kuma Geidam a Jihar Yobe.
A lokacin wannan aiki, dakarun sun ƙwato wasu kayayyaki da suka haɗa da mota, babur, wayoyin salula, fasfo na ƙasar China, da kuma kuɗi Naira 10,000.
Shugaban sashen yaɗa labaran tsaro, Manjo Janar Edward Markus Kangye, ya bayyana hakan a wata ganawa da manema labarai a Abuja.
Ya ce sojojin sun kuma kai farmaki wasu yankuna bisa bayanan sirri da suka samu, ciki har da Gwoza da Abadam a Borno da kuma Nangere a Yobe, daga 6 zuwa 9 ga watan Yuni.
Ya ƙara da cewa daga 6 zuwa 11 ga watan Yuni, wasu maza da mata da yara da dama sun miƙa wuya ga dakarun Najeriya.
Kangye ya bayyana cewa rundunar ta kuma kai wasu hare-hare tare da haɗin gwiwar jami’an tsaro a Ngala, Marte, Gwoza a Jjihar Borno da Bade da Gujba a Jihar Yobe daga 6 zuwa 10 ga watan Yuni.
A wannan lokaci, sun lalata sansanonin ’yan ta’adda, sun ƙwato makamai da alburusai.
Manjo Janar Kangye ya ce sojojin Najeriya za su ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin ’yan ƙasa tare da tabbatar da doka da oda.
“Mun ƙudiri aniyar kare martabar Najeriya da tabbatar da zaman lafiya a kowane yanki na ƙasar nan. Wannan aiki namu na ci gaba da yin tasiri,” in ji shi.
Ya buƙaci haɗin kan jama’a wajen taimaka wa sojoji su ci gaba da yaƙi da ’yan ta’adda.
Ya ce idan jama’a da hukumomi suka haɗa kai, Najeriya za ta samu zama lafiya da wadata.
“Zamu ci gaba da sanar da al’umma duk wani ci gaba da muka samu wajen yaƙar ta’addanci,” in ji Kangye.