Ko Jam’iyyun Adawa Na Iya Kai Bantensu A 2027?
Published: 31st, January 2025 GMT
A kwanakin baya, jam’iyyar PDP da sauran jam’iyyun adawa sun zargi APC da ruruta wutar rikicin da ke tsakaninsu, inda suka yi zargin cewa jam’iyya mai mulki na neman murkushe ‘yan adawa domin tabbatar da ci gaba da mulkin Shugaba Tinubu a 2027. APC ta musanta wadannan ikirari.
Tun da aka hambarar da jam’iyyar PDP, jam’iyyun adawa sun yi yunkuri da dama amma ba su samu nasara ba.
Kafin wannan, a shekarar 2018, jam’iyyar PDP ta kulla kawance da wasu jam’iyyun siyasa 38, inda suka sanya mata suna ‘Coalition of United Political Parties’ (CUPP) a wani taro da aka gudanar a cibiyar Musa Yar’adua da ke Abuja. Wannan gamayyar dai ta yi nufin kayar da tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari da jam’iyyar APC a zaben 2019. Shugabannin jam’iyyun ADC, SDP, NCP, LP, da sauran jam’iyyu da dama da suka yi rajista sun halarci taron.
Sai dai kawancen ta kasa hana Buhari sake lashe zabe, saboda rashin kokarin habaka dimokuradiyya na samun goyon bayan ‘yan Nijeriya.
A ranar 6 ga Disamba, 2023, PDP, NNPP da wasu jam’iyyun siyasa biyar suka kafa sabuwar kawance. Jam’iyyun da abin ya shafa sun hada da ADC, APM, SDP, YPP da ZLP.
Wannan sabon yunkuri mai suna ‘Coalition of Concerned Political Parties’ (CCPP), an kafa shi ne a sakatariyar jam’iyyar SDP ta kasa da ke Abuja. Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar, ya bukaci jam’iyyun adawa da su hada kai a yunkurin kwace mulki daga hannun APC.
A ranar 12 ga Disamba, 2024, jam’iyyar PRP ta tabbatar da cewa ta fara tattaunawa da jam’iyyar ADC gabanin zaben 2027.
Shugaban jam’iyyar PRP na kasa, Falalu Bello ya tabbatar da tattaunawar a wani taron manema labarai na hadin gwiwa da shugaban ADC, Ralph Nwosu a Abuja. Bello ya jaddada cewa, “Mun fara tattaunawa. Ba ma tsoron hadewa kwata-kwata. Jam’iyyar PRP ita ce jam’iyyar siyasa mafi dadewa a yau, kuma muna da tarihin kawance da suka samu nasara.”
Ana ta rade-radin cewa za a raba madafun iko tsakanin Atiku, Kwankwaso da Obi, inda Atiku zai yi mulki na tsawon shekaru hudu, sai kuma Kwankwaso na wasu shekaru hudu, da Obi na tsawon shekaru takwas. Sai dai a kwanakin baya Kwankwaso ya musanta wanzuwar irin wannan yarjejeniya, inda ya bayyana hakan a matsayin kage.
Shi ma ya musanta wata tattaunawa na hadewa ko yarjejeniyar siyasa da PDP, NNPP ko wata jam’iyya.
Wani mai sharhi kan harkokin siyasa, Jackson Lekan Ojo, ya yi imanin cewa jam’iyyun adawa za su iya kayar da Tinubu a 2027 idan suka yi amfani da dabaru irin na APC kafin zaben 2015. Ojo ya kara da cewa akwai batutuwa da dama a karkashin wannan gwamnati da ‘yan adawa za su iya cin gajiyarsu, da suka hada da kalubalen tsaro, tabarbarewar tattalin arziki, da kuma cin hanci da rashawa.
“Idan har jam’iyyun adawa suka hada kai suka mayar da hankali kan gazawar gwamnati mai ci, musamman matsalar tsaro da tabarbarewar tattalin arzikin kasar, za su iya samun nasara. Abu mai muhimmancin shi ne, a zakulo dan takara mai karfi wanda zai iya hada kan ‘yan adawa tare da gabatar da sahihin zabi,” in ji Ojo.
Daraktan makarantar nazarin zamantakewar siyasa ta Abuja, Dakta Sam Amadi ya yi imanin cewa hadewar jam’iyyun adawa za ta iya yin nasara idan har shugabannin ‘yan adawa suka kuduri aniyar cimma wata manufa ta ci gaban kasa tare da ajiye muradun kashin kai.
কীওয়ার্ড: tabbatar da
এছাড়াও পড়ুন:
Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan
Shugaban Masar Abdel Fattah al-Sisi ya gana da Shugaban Eritrea Isaias Afwerki domin tattauna halin da ake ciki a yankin, Shugaba al-Sisi ya tabbatar da jajircewar Masar wajen tallafawa ‘yancin kai da kuma ‘yancin yankin Eritrea.
A yayin taron, wanda Ministan Harkokin Wajen Masar Badr Abdel-Aty da takwaransa na Eritrea, Osman Saleh Mohammed suka halarta, shugabannin biyu sun tattauna halin da ake ciki a yankin.
Sun tabbatar da hangen nesansu kan hanyoyin kawo karshen yakin a Sudan, suna masu jaddada bukatar tallafawa cibiyoyin gwamnati na kasa, musamman Sojojin Sudan, tare da kin amincewa da duk wani yunkuri na kafa hukumomi ko cibiyoyi masu kishiyantar gwamnati a kasar.
Shugaba al-Sisi ya jaddada matsayar Masar da kuma kokarin da take yi don kawo karshen yakin da kuma rage wahalhalun jin kai na al’ummar Sudan, ta hanyar yin aiki tare da abokan huldar Masar don tabbatar da hadin kan Sudan, mutuncin yankin, da kuma ‘yancin kan kasa.
A nasa bangaren, Shugaba Afwerki ya nuna matukar godiyarsa ga rawar da y ace Masar tana takawa karkashin jagorancin Shugaba El-Sisi, wajen karfafa zaman lafiya da kuma kokarin ci gaban yankin kusurwar Afirka da Gabashin Afirka. Ya yi maraba da fadada hadin gwiwar tattalin arziki da Masar da kuma karfafa hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu kan batutuwan kasa da kasa da na yanki masu amfani ga junansu.
Taron ya kuma yi magana kan sabbin abubuwan da suka faru a Somaliya, inda Shugabannin biyu sun jaddada kudurin kasashensu na amincewa da sanarwar hadin gwiwa da aka fitar a taron kolin Masar, Eritrea, da Somaliya a Asmara a watan Oktoban 2014, wanda ya tabbatar da wajibcin girmama ka’idoji da dokokin kasa da kasa, musamman ma cikakken yankin Somaliya da dukkan kasashen yankin.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Kutsen Na Isra’ila A Kudancin Kasar October 31, 2025 Madagascar Ta Sanar da Kafa Sabuwar Gwamnati Tare da Manyan ‘Yan Adawa October 31, 2025 Iran ta yi fatali da kalamman IAEA Kan Shirin Nukiliyarta October 30, 2025 Trump Ya Umarci Ma’aikatar Yakin Amurka Ta koma gwajin makaman nukiliya October 30, 2025 Isra’ila ta amince da fadada matsugunai a Yammacin Kogin Jordan October 30, 2025 Gaza: hare-haren Isra’ila sun kashe mutane 100 Cikin Kwanaki Biyu October 30, 2025 Sudan : Kasashen duniya na tir da cin zarafi a El-Fasher October 30, 2025 Iran Ta Jaddada Bin Hanyar Diflomasiya Ko Da A Lokacin Yaki Ne Amma Ba Zata Amince Da Bin Umarni Ba October 30, 2025 Qalibaf: Amurka Tana Yaudarar Duniya Da Zaman Lafiya, Alhalin Tana Ci Gaba Da Kai Harin Wuce Gona Da Iri October 30, 2025 Ci Gaba Da Killace Gaza Bayan Tsagaita Bude Wuta Ya Janyo Mutuwar Mutane 1000 A Yankin October 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci