Leadership News Hausa:
2025-06-15@13:22:15 GMT

NPA Da Kamfanin NLNG Za Su Kulla Hadakar Fitar Da Iskar Gas Ketare

Published: 31st, January 2025 GMT

NPA Da Kamfanin NLNG Za Su Kulla Hadakar Fitar Da Iskar Gas Ketare

“Kamafanin na LNG na kasa, na bayar da gagarumar gudunmawa wajen bunkasa tattalin azrikin Nijeriya da kuma kara bayar da goyon baya wajen ganin ana fitar da kaya zuwa ketare, kuma zamu tabbatar da cewa, an kara karfafa hadaka a tsakanin Hukumar da Kamfanin.” Inji Dantsoho.

“Rarar da Nijeriya ta samu na hada-hada ta kai ta Naira tiriliyan 5.

81 wacce ta yi daidai da dala biliyan 3.7, a zango na uku hudu a 2024.” Kamar yadda rukunonin taron bunkasa tattalin arziki na Nijeriya NESGya ruwaito.

Rahoton ya sanar da cewa, an samu wannan nasarar ce, biyo bayan amfanin da Tashoshin Hukumar Jiragen Ruwa ta Kasa NPA.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Mulkin Tinubu ya fi kowane muni tun bayan dawowar mulkin farar hula — Dalung

Tsohon Ministan Matasa da Wasanni, Solomon Dalung, ya ce shekara biyu da Bola Ahmed Tinubu ya yi a matsayin shugaban ƙasa sun fi kowane lokaci muni tun bayan dawowar mulkin dimokuraɗiyya a ƙasar.

Yayin da yake magana da BBC a ranar Dimokuraɗiyya da Najeriya ke cika shekaru 26 tana mulkin farar hula, Dalung ya ce ba wani abin arziƙi da talaka ya amfana da shi daga wannan gwamnati.

An kama ’yar Najeriya da laifin safarar ɗalibai 15 a Australia Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi

Ya ce: “Kawai abin da talaka ya samu daga gwamnatin Tinubu shi ne tsadar rayuwa, yunwa, wahala da matsalar tsaro.”

Ya zargi gwamnatin da cewa cire tallafin man fetur ba tare da shiri ba, kuma hakan ya jefa mutane cikin ƙuncin rayuwa.

“Talakawa na mutuwa saboda yunwa, amma idan an tambayi Shugaba Tinubu, sai ya ce bai yi nadamar cire tallafin ba,” in ji Dalung.

Gwamnatin Tinubu dai ta ce ta cire tallafin ne domin hana wasu tsiraru ci gaba da cin gajiyarsa da kuma bunƙasa tattalin arziƙin ƙasa.

Amma Dalung ya ce gwamnatin ba ta talaka ta ke ba: “Idan ba canza motoci da jirage da gina sabon gida ga mataimaki ba, to babu wani abu da talaka ya gani.”

Dalung ya ce dimokuraɗiyya na cikin mawuyacin hali tun zuwan Tinubu, ya zargi gwamnati da kama waɗanda ke sukar ta da kuma sayen abokan hamayya wajen komawa APC.

“Mun ga yadda ake kama ‘yan gwagwarmaya saboda kawai sun faɗi ra’ayinsu. Kuma wasu na komawa jam’iyyar APC bayan an saye su,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa gwamnati na barazana ga ci gaban ƙasa idan ba a gyara lamarin ba.

Dalung, ya ce duk da rahoton Bankin Duniya da ke cewa tattalin arziƙin Najeriya na bunƙasa, bai yarda ba.

“Ta yaya za ku ce tattalin arziƙin da ke cikin matsin lamba yanzu yana bunƙasa? Wannan fa ba gaskiya ba ce.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An samu gobara a wasu matatun mai guda biyu na Iran bayan harin da Isra’ila ta kai
  • An Samu Babban Canji Kan Tsarin Ciniki A Tsakanin Sin Da Afirka
  • Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025
  • Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai
  • Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
  • Mulkin Tinubu ya fi kowane muni tun bayan dawowar mulkin farar hula — Dalung
  • Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: An Yi Kira Ga Amurka Da Ta Cimma Daidaito Da Sin Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya
  • An Bude Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afirka A Changsha
  • Aliko Dangote Ya Sauka Daga Shugabancin Kamfanin Sukarin Dangote