Aminiya:
2025-06-15@13:10:03 GMT

Direba cikin barasa ya murƙushe sojoji sun mutu a Legas

Published: 31st, January 2025 GMT

Wasu sojoji da har yanzu ba a tantance adadinsu ba sun mutu yayin da wasu suka samu raunuka bayan da wani da ake zargin wani direba da ya bugu cikin barasa ne ya kutsa cikin su a yankin Shomolu da ke Jihar Legas.

Lamarin ya faru ne ’yan mintuna kaɗan bayan da sojojin suke kan hanyarsu daga Barikin Myoung da ke yankin Marocco a Shomolu.

Ya tona kabarin mijin mahaifiyarsa ya yanke kansa a Adamawa Matashi ya yi lalata da ’yan firamare biyu a Zariya

Waɗanda suka samu raunuka suna jinya a asibitin sojojin Nijeriya da ke Yaba, yayin da aka ajiye gawarwakin sojojin da suka rasu a ɗakin ajiye gawa a asibitin.

Hedikwatar Runduna ta 81 ta Sojojin Nijeriya, ta sanar a ranar Alhamis cewa za ta fara gudanar da tattakinta a yankin na farko, na kowace shekara a yau Juma’a.

Tattakin mai tsawon kilomita 15, wanda aka dakatar sakamakon wannan mummunan al’amari, ya kamata ya ratsa sassan babban yankin da tsibirin Legas.

Sanarwar ta kuma gargaɗi mazauna yankin da su kwantar da hankulan su domin tattakin da aka saba yi na atisayen soji ne.

Wata majiyar soji ta ce motar ta kutsa cikin taron sojojin, inda ta kashe wasu daga cikin su nan take.

Majiyar ta kuma bayyana cewa, tun daga lokacin aka kama direban.

Sai dai majiyar ba ta bayyana inda ake tsare da mutumin domin amsa tambayoyi ba.

Wani ganau ya ce, “Tattakin hanyar ya tsaya kwatsam sakamakon lamarin. Ba zan iya bayar da cikakken bayani kan adadin waɗanda suka mutu ba, amma sojoji da dama sun samu munanan raunuka yayin da wasu ’yan ƙalilan suka mutu.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yaba

এছাড়াও পড়ুন:

Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe

Rundunar ’Yan Sandan jihar Gombe, ta tabbatar da mutuwar mutum biyar da kuma jikkatar wasu 13, sakamakon tashin wutar lantarki a unguwar Tudun-Wada, Pantami a jihar.

Wutar ta tashi ne da safiyar ranar Asabar sakamakon matsala da ta taso daga wata tiransifoma a yankin, kamar yadda kakakin ’yan sandan jihar, DSP Buhari Abdullahi, ya bayyana.

Sojoji sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa

Cikin waɗanda suka rasa rayukansu har da Babban Sakatare na Ma’aikatar Ayyuka ta Musamman ta jihar, Alhaji Muhammad Yusuf Kulani, tare da ’ya’yansa da wasu mazauna unguwar.

Marigayin shi ne shugaban ƙungiyar ƙwararrun akantoci ta Jihar Gombe (ANAN).

’Yan sanda daga ofishin Low-Cost sun isa wajen don tabbatar da tsaro da kuma kai waɗanda suka jikkata zuwa asibiti.

Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, Bello Yahaya, ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan mamatan.

Ya kuma ce za su gudanar da cikakken bincike domin gano musabbabin tashin wutar da kuma ɗaukar matakan kare faruwar hakan a gaba.

Ya kuma roƙi al’umma da su kasance masu bin doka tare da bayar da haɗin kai yayin gudanar da binciken.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An samu gobara a wasu matatun mai guda biyu na Iran bayan harin da Isra’ila ta kai
  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
  • Dakarun Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Kakkabo Jiragen Yakin Isra’ila Biyu Kirar F-35
  • Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Kamfanonin Waje Sun Ce Dole Ne Su Shiga A Dama Da Su A Cikin Kasuwar Kasar Sin
  • Harin Isra’ila a kan Iran ya jefa yankin Gabas ta Tsakiya cikin zama dar-dar
  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara
  • Sojoji Sun Kashe Auta, Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda Da Wasu 13 a Jihar Zamfara