Direba cikin barasa ya murƙushe sojoji sun mutu a Legas
Published: 31st, January 2025 GMT
Wasu sojoji da har yanzu ba a tantance adadinsu ba sun mutu yayin da wasu suka samu raunuka bayan da wani da ake zargin wani direba da ya bugu cikin barasa ne ya kutsa cikin su a yankin Shomolu da ke Jihar Legas.
Lamarin ya faru ne ’yan mintuna kaɗan bayan da sojojin suke kan hanyarsu daga Barikin Myoung da ke yankin Marocco a Shomolu.
Waɗanda suka samu raunuka suna jinya a asibitin sojojin Nijeriya da ke Yaba, yayin da aka ajiye gawarwakin sojojin da suka rasu a ɗakin ajiye gawa a asibitin.
Hedikwatar Runduna ta 81 ta Sojojin Nijeriya, ta sanar a ranar Alhamis cewa za ta fara gudanar da tattakinta a yankin na farko, na kowace shekara a yau Juma’a.
Tattakin mai tsawon kilomita 15, wanda aka dakatar sakamakon wannan mummunan al’amari, ya kamata ya ratsa sassan babban yankin da tsibirin Legas.
Sanarwar ta kuma gargaɗi mazauna yankin da su kwantar da hankulan su domin tattakin da aka saba yi na atisayen soji ne.
Wata majiyar soji ta ce motar ta kutsa cikin taron sojojin, inda ta kashe wasu daga cikin su nan take.
Majiyar ta kuma bayyana cewa, tun daga lokacin aka kama direban.
Sai dai majiyar ba ta bayyana inda ake tsare da mutumin domin amsa tambayoyi ba.
Wani ganau ya ce, “Tattakin hanyar ya tsaya kwatsam sakamakon lamarin. Ba zan iya bayar da cikakken bayani kan adadin waɗanda suka mutu ba, amma sojoji da dama sun samu munanan raunuka yayin da wasu ’yan ƙalilan suka mutu.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yaba
এছাড়াও পড়ুন:
Sojan Amurka Ya Bada Ruwayar Yadda Sojojin Sahayoniyya Suka Kashe Wani Yaro Balasdine
Wani sojan Amurka ya ba da shaida game da kisan wani yaro da sojojin mamayar Isra’ila suka yi a cibiyar bada agaji ta Rafah
Wani sojan Amurka da ke aiki a cibiyar rarraba kayan abinci a zirin Gaza ya yi furuci da cewa: Sojojin mamayar Isra’ila sun kai hari kan wani yaro Bafalasdine da ya yi tafiya mai nisan kilomita 12 a karkashin zafin rana, don neman kayan abincin agaji a yankin.
A cikin wata sheda mai ratsa jiki da ya bayar a cikin wani dan gajeren faifan bidiyo a Amurka, Private Anthony Aguilar ya ba da labarin wani lokaci da ba za a manta da shi ba cewa: Wani yaro siriri mai suna Amir, babu takalmi a kafarsa, ya yi tafiya mai nisa don isa wurin rarraba kayan agaji inda aka ba shi shinkafa da adasi inda ke ja a kasa.
Sojan Amurkan nan ya kara da cewa: Yaron nan ya matso kusa da shi, ya sumbaci hannunsa, ya ce, “Na gode.”
Bayan ‘yan mintoci, yayin da Amir ke tafiya tare da wasu fararen hula, sai sojojin mamayar Isra’ila sun harba barkonon tsohuwa da harsasai kan taron jama’ar, inda suka raunata Falasdinawa masu yawa tare da kashe Amir nan take.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Sojojin Yemen Sun Kai Zafafan Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila Guda Uku July 31, 2025 Qolibaf: Barin HKI Ta Yi Abinda Taga Dama Ne Yana Karfafa Mata Giwa July 30, 2025 Yunwa Ta Kashe Karin Falasdinawa 7 A Gaza July 30, 2025 Malta Zata Amince da Samuwar Falasdinu a Cikin Watan Satumba Mai Zuwa July 30, 2025 Amurka Ta Ce HKI Ba Zata Fice Daga Kasar Lebanon Ba Sai An Kwance Damarar Hizbullah July 30, 2025 Siriya Da HKI Zasu Gudanar Da Taro A Baku July 30, 2025 Girgizar Kasa Mai Karfi Ta Kada Yankin Kamtashatka Na Kasar Rasha July 30, 2025 Yahudawa ‘Yan Share Wuri Zauna Sun Kutsa Cikin Masallacin Kudus July 30, 2025 Kasashen Yankin Caribbean Suna Son Bunkasa Alakarsu Ta Kasuwanci Da Nahiyar Afirka July 30, 2025 Shugaban Kasar Ivory Coast Ya Bayyana Shirinsa Na Sake Tsayawa Takarar Shugabanci Karo Na Hudu July 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci