Aragchi Yace Duk Wani Harin Da Aka Kaiwa Cibiyoyin Nukliyar Kasar Iran Hakan Wata Musiba ce Ga Yankin Asiya Ta Yamma
Published: 28th, January 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa duk wani hari kan daya daga cikin cibiyoyin Nukliyar kasar Iran daga HKI ko Amerika, wannan wata musiba ce da yankin, kuma wadanda suka kai harin zasu gamu da maida martani ba tare da jinkiri ba.
Tashar talabijin ta Presstva nan Tehran ta nakalto Abbas Aragchi yana fadar haka a wata hirar da ta hada shi da tashar talabijin ta Sky News a nan Tehran.
Ya kuma kara da cewa, ban tsamman zasu yi haka ba. Amma idan sun, to kuwa ba zasu ji ta da dadi ba.
Yace: JMI ta rattaba hannu a kan yarjeniyar Nukliya da manya-manyan kasashe 6 a duniya kan shirin ta na makacin Nukliya wanda ake fi sani da JCPOA amma a shekara ta 2018 shugaba Trump a wa’adin mulkinsa na farko ya fitar da Amurka cikin yarjeniyar, sannan ya dora mata takunkuman arziki mafi muni a tarihin kasar Iran, da nufin karya gwamnatin JMI. Amma hakan bai faru ba. Sai kuma a shekara ta 2019 Iran ta fara dauke kataita shirin makamashin nukliyarta ta zaman lafiya da ta saboda maida martani ga dayan bangaren wacce ta sabawa alkawulanta su.
A baya-bayan nan mun ji Trump yana fadin wasu maganganu, wanda yake cewa masu dadi, amma sai mun ganshi a kasa. Sai dai yakamata Amurka da kawayenta su sani ka cewa Iran ba zata sake tattaunawa da su da sauki ba.
Daga karshe ministan ya mayarwa Trump Martani kan mutanen gaza, da cewa ya maida HKI zuwa Green Island ya fi mata sauki da ya maida Falasdinawa Masar da Jordan.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran ta damu da halin da ake ciki a yankin El Fasher na Sudan
Jamhuriyar Musulinci ta Iran, ta nuna damuwarta game da irin tashin hankali da ake ciki a Sudan musamman a yankin El Fasher.
Iran ta sake jaddada goyon bayanta ga ‘yancin Sudan, da hadin kai, da kuma cikakken yankin kasar yayin da tashin hankali ya mamaye kasar dake Arewacin Afirka.
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araghchi ne ya bayyana hakan yayin wata tattaunawa ta waray tarho da takwaransa na Sudan Mohiuddin Salem a ranar Juma’a.
Na farko ya nuna damuwa musamman game da hare-hare da kisan gillar da aka yi wa fararen hula a birnin El Fasher da ke kudu maso yammacin Sudan.
Duniya ta damu matuka a daidai lokacin da ake ci gaba da samun karuwar tashin hankali a Sudan.
A ranar Talata, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esmaeil Baghaei ya bayyana matukar damuwa game da rikice-rikicen makamai da ake ci gaba da yi a El Fasher, yana mai Allah wadai da lalata kayayyakin more rayuwa da kuma kisan fararen hula a birnin.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara November 1, 2025 Samia Suluhu Hassan ta lashe zaben shugaban kasa a Tanzaniya November 1, 2025 Najeriya ta musanta ikirarin Trump, na cewa Kristoci na fuskantar babbar barazana a kasar November 1, 2025 Majalisar Dinkin Duniya ta damu da hare-haren Amurka a Caribbean da Pacific November 1, 2025 Israila Ta Kai Hari Kan Ofishin kungiyar UNICEF Dake Gaza A November 1, 2025 Amurka Na Shirin Kai Hari Kan Kasar Venzuwela A Kowanne Lokaci November 1, 2025 Iran Ta Sanya Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3 October 31, 2025 Isra’ila Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza October 31, 2025 An Tube Yarima Mai Jiran Gado Na Birtaniya Bayan Da Aka Tabbatar Da Laifinsa October 31, 2025 Kasashen Pakistan Da Afghanistan Sun Tsawaita Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta October 31, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci