Leadership News Hausa:
2025-05-01@01:05:19 GMT

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutum 4 Ƴan Gida Ɗaya A Abuja

Published: 28th, January 2025 GMT

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutum 4 Ƴan Gida Ɗaya A Abuja

Rundunar ƴansandan Abuja, ta bayyana cewa rashin samun labarin lamarin da wuri ne ya kawo jinkirin ɗaukar mataki.

Mun Fara Bincike – Ƴansanda

Kakakin rundunar ƴansandan Abuja, Josephine Adeh, ta tabbatar da faruwar lamarin, inda ta ce tuni suka fara bincike domin ceto waɗanda aka yi garkuwa da su.

Ta ce: “Ƙarfe 1 na dare muka samu kiran gaggawa cewa ƴan bindiga sun kai hari Chikakore.

Nan take muka tura ƴansanda zuwa yankin. Bincike ya nuna cewa maharan guda bakwai ne, sun yaudari mai gidan har ya buɗe musu ƙofa.”

Ta kuma ce wata maƙwabciyarsu da ta yi ƙoƙarin taimaka musu ta ji rauni, kuma tana karɓar magani a asibiti.

Rundunar ta buƙaci mazauna yankin su kwantar da hankalinsu tare da bayar da haɗin kai wajen bincike.

Fargaba Kan Matsalar Tsaro a Abuja

Wannan harin ya jefa tsoro a zukatan mazauna yankin, musamman waɗanda suka sha fama da matsalolin tsaro a baya.

A farkon watan nan, wasu ƴan bindiga da ake sun tayar da abun fashewa a wata makarantar Islamiyya a ƙauyen Kuchibuyi, Bwari, inda mutane biyu suka rasa rayukansu.

Yankin Bwari, wanda ke maƙwabtaka da jihohin Kaduna da Neja, ya sha fama da hare-haren ƴan bindiga, ciki har da sace mutane domin neman kuɗin fansa.

Wannan ya sa mazauna yankin ke fargabar dawowar zaman ɗar-ɗar a rayuwarsu.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Hari Yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Talata ce ɗaya ga watan Zhul Qi’ida — Sarkin Musulmi

Sarkin Musulmi, Alhaji Abubakar Muhammad Sa’ad, ya bayyana cewa gobe Talata, 30 ga watan Afrilun 2025, ita ce za ta kasance 1 ga watan Zhul Qi’ida na shekarar 1446 ta Hijiriyya.

Wata sanarwa da shugaban kwamatin ganin wata na fadar, Farfesa Sambo Wali ya fitar ta ce an ɗauki matakin ne saboda ba a ga jinjirin watan ba a ranar Lahadi.

Yadda matar gwamna ta sa mata gasar haihuwar ’yan uku Rasha ta ayyana tsagaita wuta ita kaɗai a yakinta da Ukraine

Hakan na nufin yau Litinin, 28 ga watan Afrilu ne 30 ga watan Ƙaramar Sallah na Shawwal.

A ƙa’idar kalandar Musulunci, kowane wata yana yin kwana 29 ne, amma idan ba a ga jaririn watan ba sai a cika shi zuwa kwana 30.

Aminiya ta ruwaito cewa tun a ranar Asabar da ta gabata ce Fadar Sarkin Musulmin ta ba da umarnin duban watan na Zhul Qi’ida.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda ’yan Tifa da baƙin direbobi ke haddasa haɗari a Abuja
  • Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga , Sun Ceto Fasinjoji 6 A Taraba
  • ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno
  • Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Sojoji Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace, Sun Ƙwato Shanu 32 A Katsina
  • Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno
  • Talata ce ɗaya ga watan Zhul Qi’ida — Sarkin Musulmi
  • Jiragen Yakin Amurka Sun Kashe Mutane Da Dama A lardin Sa’ada Na Kasar Yemen
  • Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci Ta Yaba Wa Gwamna Lawal Kan Matakan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara