Leadership News Hausa:
2025-06-15@06:51:53 GMT

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutum 4 Ƴan Gida Ɗaya A Abuja

Published: 28th, January 2025 GMT

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutum 4 Ƴan Gida Ɗaya A Abuja

Rundunar ƴansandan Abuja, ta bayyana cewa rashin samun labarin lamarin da wuri ne ya kawo jinkirin ɗaukar mataki.

Mun Fara Bincike – Ƴansanda

Kakakin rundunar ƴansandan Abuja, Josephine Adeh, ta tabbatar da faruwar lamarin, inda ta ce tuni suka fara bincike domin ceto waɗanda aka yi garkuwa da su.

Ta ce: “Ƙarfe 1 na dare muka samu kiran gaggawa cewa ƴan bindiga sun kai hari Chikakore.

Nan take muka tura ƴansanda zuwa yankin. Bincike ya nuna cewa maharan guda bakwai ne, sun yaudari mai gidan har ya buɗe musu ƙofa.”

Ta kuma ce wata maƙwabciyarsu da ta yi ƙoƙarin taimaka musu ta ji rauni, kuma tana karɓar magani a asibiti.

Rundunar ta buƙaci mazauna yankin su kwantar da hankalinsu tare da bayar da haɗin kai wajen bincike.

Fargaba Kan Matsalar Tsaro a Abuja

Wannan harin ya jefa tsoro a zukatan mazauna yankin, musamman waɗanda suka sha fama da matsalolin tsaro a baya.

A farkon watan nan, wasu ƴan bindiga da ake sun tayar da abun fashewa a wata makarantar Islamiyya a ƙauyen Kuchibuyi, Bwari, inda mutane biyu suka rasa rayukansu.

Yankin Bwari, wanda ke maƙwabtaka da jihohin Kaduna da Neja, ya sha fama da hare-haren ƴan bindiga, ciki har da sace mutane domin neman kuɗin fansa.

Wannan ya sa mazauna yankin ke fargabar dawowar zaman ɗar-ɗar a rayuwarsu.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Hari Yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Guguwa ta hallaka mutum 6, ta jikkata 30 a Taraba

Wata mummunar guguwa ta yi sanadin mutuwar mutum shida sannan ta jikkata wasu 30 a garin Garba-Chede da ke karamar hukumar Bali a jihar Taraba.

A cewar wani mazaunin yankin wanda guguwar ta lalata wa gida mai suna Abubakar Dodo, an shafe shekaru masu yawa ba su ga irin ta ba a yankin saboda munin barnar da ta yi.

Rashin wutar lantarki ya durƙusar da kasuwanci a Arewa Maso Gabas An kashe jaririn wata 9 da wasu 3 a Filato

A cewarsa, ban da gidaje, guguwar ta kuma lalata makarantu da masallatai da coci-coci, sannan kayan abinci na miliyoyin Naira sun salwanta.

Dagacin garin na Garba-Chede, Kaigama Maigandi, ya yi kira ga Gwamnan Jihar, Agbu Kefas, da ya taimaka wa mutanen yankin da iftila’in ya shafa domin su samu su gyara gidaje da wuraren kasuwancinsu.

A wani labarin kuma, wata tawagar wakilai daga Hukumar Raya Yankin Arewa Maso Gabas (NEDC), ta ziyarci yankin domin jajanta musu da kuma ganin girman barnar domin ganin irin tallafin da za a yi musu.

Ayarin, wanda ke karkashin jagorancin Dr. Balutu Isa Mohammed, ya yi jaje ga mutanen tare da yi musu alkawarin ba su tallafin muhimman abubuwan da suke bukata domin su rage radadi.

Tawagar ta kuma ziyarci Dagacin garin tare da yi masa bayanin musabbabin zuwansu da kuma ayyukan da suke yi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina
  • Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna
  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara
  • Mutum ɗaya ya tsira da ransa cikin 242 a hatsarin jirgin India
  • Guguwa ta hallaka mutum 6, ta jikkata 30 a Taraba
  • EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Zargi Aikata Damfara A Intanet A Kaduna
  • Basaraken Da Aka Sace A Kogi Ya Kuɓuta Bayan Shafe Kwanaki 27 A Hannun ‘Yan Bindiga 
  • An kashe mutum 41 cikin mako ɗaya a Filato