Babban sakataren kungiyar Hizbullahi ta kasar Lebanon ya ce: Batun rusa gwagwarmaya ta zama tatsuniya kuma batun Falasdinawa ya dawo cikin fagen siyasar duniya

Babban sakataren kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hizbullah ta kasar Lebanon, Sheikh Na’im Qassem ya jaddada cewa: Harin daukan fans ana “Ambaliyar Al-Aqsa” ta cimma burinta na mayar da al’ummar Falastinu a fagen kasa da kasa, yana mai cewa; Gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta zame a matsayin kungiyar ta’addanci ta masu aikata laifuka da kisa kiyashi a idon duniya.

Babban sakataren kungiyar ta Hizbullah Sheikh Na’im Qasem ya bayyana a wani jawabi da ya gabatar a yammacin jiya Litinin game da sabbin abubuwan da ke faruwa a kasar Lebanon da kuma yankin, inda ya ce: “Hare-haren wuce gona da iri kan kasar Lebanon, kamar Gaza, cin zarafi ne da suka faru tare da cikakken goyon bayan Amurka da kasashen yammacin duniya da ba sa bin doka da oda. kuma suna aiwatar da kashe-kashen gilla kan fararen hula tare da lalata duk wani abin more rayuwa ba tare da wata damuwa ko kulawa ba.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Lebanon

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Sandan Niger Sun Hada ‘Yan’uwa Mutanen 35 Da Aka Ceto Da Iyalansu 

Rundunar ‘yan sandan jihar Neja ta saki tare da hada wadanda aka yi garkuwa da su talatin da biyar tare da iyalansu.

 

Sun kunshi mata goma sha shida da yara goma sha tara daga Kagara, Tegina da Agwara, bayan sun shafe makonni a hannun ‘yan sanda da ke tsare da kuma kawar da hankalinsu daga barayin da ke Minna.

 

Kwamishinan ‘yan sanda mai kula da jihar Neja Adamu Abdullahi Elleman ya bayyana haka a lokacin wani takaitaccen bayani da ya mikawa shugaban karamar hukumar gidan rediyon Ayuba Usman Katako a Minna.

 

Kwamishinan ‘yan sandan wanda mataimakin kwamishinan ‘yan sanda Ibrahim Adamu ya wakilta, ya bayyana cewa za’a sake haduwa da wadanda abin ya shafa da iyalansu domin sun kasance karkashin kulawar ‘yan sanda tare da tallafi da kulawar da suka dace daga gwamnatin jihar Neja.

 

A cewarsa, hakan ya fara ne a ranar 3 ga watan Yulin 2025 lokacin da aka samu labari daga wata majiya mai tushe da ke nuna cewa wadanda abin ya shafa na kaura daga Birnin-Gwari a jihar Kaduna zuwa wasu yankuna.

 

Jami’an ‘yan sanda sun yi kaca-kaca da rukunin farko na st Agwara a kokarin da suke na tsallakawa kogin zuwa wasu kauyukan New-Bussa na jihar Neja tare da ceto mata biyar da kananan yara shida.

 

A yayin da ake gudanar da tambayoyi, an bayyana cewa ‘yan bindigar na yin kaura daga Birnin-Gwari zuwa wasu unguwanni kuma rundunar ‘yan sandan da ke aiki a hanyar Mekujeri zuwa Tegina ta cafke kashi na biyu tare da mata hudu da kananan yara bakwai, yayin da kuma aka kama wani rukunin tare da direban da ya tafi da su.

 

Bincike ya nuna cewa direban, Yusuf Abdullahi na Birnin-Gwari ya je sansaninsu ne domin kai mutanen da abin ya shafa, kuma yana kan bincike don tabbatar da hadin gwiwarsa a ayyukansu.

 

Kwamishinan ‘yan sandan, Adamu Abdullahi Elleman, ya tabbatar da cewa tun da aka tsare wadanda abin ya shafa, an ba su wasu shawarwari da nasiha, da abinci da kuma kayan kwanciya.

 

Ya kara da cewa, bayan samun takardar izinin da ya kamata, ana mika wadanda abin ya shafa ga shugaban karamar hukumar da ‘yan uwansu tare da yin kira ga jama’a da su baiwa ‘yan sanda bayanan da suka dace a duk lokacin da aka lura da al’amura domin gaggauta shiga tsakani.

 

PR ALIYU LAWAL.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Shugaban Kasar Lebanon Aun Ya Ce Mun Aike Wa  Amurka Sakwanni Akan Dakatar Da Hare-haren HKI
  • Kassim: Duk Wanda Yake Neman Hizbullah Ta Ajiye Makamanta Yana Yi Wa Isra’ila Aiki
  • ‘Yan Sandan Niger Sun Hada ‘Yan’uwa Mutanen 35 Da Aka Ceto Da Iyalansu 
  • Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega
  • Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya
  • Amurka Ta Ce HKI Ba Zata Fice Daga Kasar Lebanon Ba Sai An Kwance Damarar Hizbullah
  • Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 
  • Kasashen Iran Da Rasha Sun Tattauna Batun Hadin Gwiwar Kafofin Watsa Labarai A Tsakaninsu
  • Hamas: HKI Da Amurka Sun Janye Daga Tattaunawa Ne Don Sake Damarar Yaki
  • Iran Ta Ce Amurka Ce Bayan Hare-haren Da Aka Kai Zahidan