Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Zai Gana Da Jami’an Iran Da Jakadojin Kasashen Musulmi
Published: 28th, January 2025 GMT
Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran zai karbi bakwancin tawagar jami’an kasar da jakadun kasashen musulmi
A cikin sa’o’i masu zuwa ne Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran Ayatullah Sayyid Ali Khamenei zai karbi bakwancin wasu tawagogin jami’an kasar, baya ga wakilai da jakadun kasashen musulmi.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo cewa: Wannan taro ya zo ne domin murnar tunawa da zagayowar ranar aiko fiyayyen halitta, Manzon Tsira Muhammadu dan Abdullahi (s.a.w) da sakon addinin Musulunci ga dukkan talikai wanda ya yi daidai da yau Talata 28 ga watan Janairu, kuma daidai da ranar 27 ga watan Rajab shekara ta 1446 bayan hijira.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
Cikin jadawalin GII na 2025, kasashe masu karanci da matsakaicin kudin shiga 17, sun taka rawar gani fiye da yadda aka yi hasashe, bisa matsayin ci gabansu, yayin da kasashen Afirka dake kudu da hamadar Sahara ke kan gaba, cikin kasashe mafiya samun ci gaban kirkire-kirkire, inda kasashen Afirka ta Kudu, da Senegal da Rwanda ke kan gaba a jerin kasashen shiyyar. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp