Gwamna Mohammed Umar Bago na jihar Neja ya bayyana cewa gwamnatin jihar na hada rijistar manoma da masu rike da mukaman siyasa a cikin shirinta na inshorar lafiya domin tabbatar da ayyukan kiwon lafiya ga daukacin ‘yan kasa.

 

Gwamnan ya bayyana haka ne a Minna, a lokacin da ya karbi bakuncin abokan hulda na ci gaba daga kungiyar Global Alliance for Vaccine Immunisation GAVI, UNICEF da WHO da suka je jihar domin bikin rufe taron GAVI da ke tallafawa tsarin karfafa tsarin PHC a jihar Neja.

 

Umar Bago ya ce manoma da masu rike da mukaman siyasa da makiyaya za a yi musu rajista ta ma’aikatar makiyaya sannan ya nuna cewa duk ma’aikatan gwamnati da masu rike da mukaman siyasa za a yi musu rajista kari akan wasu su dubu dari biyu da hamsin da suka rigaya.

 

Gwamnan ya kuma jaddada aniyar gwamnatinsa na ci gaba da yin rijistar haihuwar yara bisa manufofin shirin na UNICEF.

 

Sai dai ya bayyana cewa nan da watanni 6 ne za a kaddamar da shirin samar da allurar riga-kafi, domin ba da damar samar da magunguna na zamani zuwa yankunan masu nisa da lungunan jihar.

 

Shugaban Hukumar Kula da Yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF, Ibrahim Sesay ya bayyana shirin rajistar haihuwa a matsayin na asali ga kowane yaro wanda shine dalilin da ya sa aka samu rijistar haihuwa dari bisa dari a shekarar 2024 tare da yiwa yara sama da 400,000 ‘yan kasa da shekaru 5 rijista.

 

Shugaban hukumar UNICEF a Najeriya Dr. Shyam Pathak ya yarda cewa shirin na shekaru 3 a jihar ya taimaka matuka wajen rage mace-mace da cututtuka ciki har da inganta samar da ayyukan kiwon lafiya ga marasa galihu.

 

Muhimman abubuwan da suka faru a wajen taron sun hada da bayar da lambar yabo ta UNICEF ga Gwamna Mohammed Umar Bago saboda gudunmawar da ya bayar a fannin kiwon lafiya.

 

KARSHEN ALIYU LAWAL/Wababe

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Inshora

এছাড়াও পড়ুন:

Binciken Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Cin Zali Ta Hanyar Kakaba Haraji Ya Illata Kimar Amurka

 

Cikin adadin, masu bayyana ra’ayoyi daga kasashen Saudiyya da Serbia, suna cikin mafiya bayyana matukar baiken matakin na Amurka, da karin kaso 28.5 bisa dari. Yayin da a daya bangaren al’ummun Malaysia, da Isra’ila, da Australia, da Singapore, da Philippines, da Najeriya, da Portugal, da Pakistan, da Afirka ta kudu, kasonsu na nuna baiken matakan kara harajin na Amurka ya karu da sama da kaso 20 bisa dari.

(Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Binciken Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Cin Zali Ta Hanyar Kakaba Haraji Ya Illata Kimar Amurka
  • Tarayyar Afirka ta dage takunkumin da ta kakabawa Gabon
  • Hajj 2025: Kaduna Ta Gaddamar Da Ayarin Likitoci Da Za Su Kula Da Alhazan Jihar
  • Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok
  • Hajjin 2025: An Fara Yi Wa Maniyyata Allurar Rigakafi A Jigawa
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Ci Gaba Da Killace Gaza Da Kashe Mutane, Laifi Ne Da Ba A Taba Yin Irinsa Ba
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Jaddada Wajabcin Komawa Kan Shirin Tsagaita Bude Wuta A Gaza
  • Akwai Ƙarin Gishiri A Yawan  Masu Sauyin Jam’iyya Zuwa APC – El-Rufai
  • Iran Da Rasha Sun Jaddada Yin Aiki Tare A Fagen Kiwon Lafiya
  • NAJERIYA A YAU: “Dalilin da muke sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki”