Gwamna Mohammed Umar Bago na jihar Neja ya bayyana cewa gwamnatin jihar na hada rijistar manoma da masu rike da mukaman siyasa a cikin shirinta na inshorar lafiya domin tabbatar da ayyukan kiwon lafiya ga daukacin ‘yan kasa.

 

Gwamnan ya bayyana haka ne a Minna, a lokacin da ya karbi bakuncin abokan hulda na ci gaba daga kungiyar Global Alliance for Vaccine Immunisation GAVI, UNICEF da WHO da suka je jihar domin bikin rufe taron GAVI da ke tallafawa tsarin karfafa tsarin PHC a jihar Neja.

 

Umar Bago ya ce manoma da masu rike da mukaman siyasa da makiyaya za a yi musu rajista ta ma’aikatar makiyaya sannan ya nuna cewa duk ma’aikatan gwamnati da masu rike da mukaman siyasa za a yi musu rajista kari akan wasu su dubu dari biyu da hamsin da suka rigaya.

 

Gwamnan ya kuma jaddada aniyar gwamnatinsa na ci gaba da yin rijistar haihuwar yara bisa manufofin shirin na UNICEF.

 

Sai dai ya bayyana cewa nan da watanni 6 ne za a kaddamar da shirin samar da allurar riga-kafi, domin ba da damar samar da magunguna na zamani zuwa yankunan masu nisa da lungunan jihar.

 

Shugaban Hukumar Kula da Yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF, Ibrahim Sesay ya bayyana shirin rajistar haihuwa a matsayin na asali ga kowane yaro wanda shine dalilin da ya sa aka samu rijistar haihuwa dari bisa dari a shekarar 2024 tare da yiwa yara sama da 400,000 ‘yan kasa da shekaru 5 rijista.

 

Shugaban hukumar UNICEF a Najeriya Dr. Shyam Pathak ya yarda cewa shirin na shekaru 3 a jihar ya taimaka matuka wajen rage mace-mace da cututtuka ciki har da inganta samar da ayyukan kiwon lafiya ga marasa galihu.

 

Muhimman abubuwan da suka faru a wajen taron sun hada da bayar da lambar yabo ta UNICEF ga Gwamna Mohammed Umar Bago saboda gudunmawar da ya bayar a fannin kiwon lafiya.

 

KARSHEN ALIYU LAWAL/Wababe

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Inshora

এছাড়াও পড়ুন:

An shawarci Manoman Kwara Da Su Yi Taka-Tsan-Tsan Saboda Hasashen Ruwa Da Tsawa A Jihar

An yi kira ga manoma a jihar Kwara da su yi taka tsan-tsan domin hasashen za a samu ruwan sama da kuma tsawa da ake hasashen nan da kwanaki masu zuwa.

 

A wata sanarwa da kwamishinan noma da raya karkara na jihar, Dr, Afees Abolore ya fitar, ya ce a cewar hukumar kula da yanayi ta Najeriya, NiMet, ana sa ran wasu sassa na jihar za su fuskanci ruwan sama da kuma yiwuwar tsawa.

 

Ya ce za a fuskanci ruwan sama ne da rana da yamma, tsakanin Litinin 28 ga Yuli da Laraba 30 ga Yuli, 2025.

 

Ya yi bayanin cewa duk da cewa ba a sami ruwan sama ba tukuna, yanayin da ke gaba zai iya kawo cikas ga ayyukan noma da ake ci gaba da yi, musamman ga masu sharefilaye, da watsin taki, ko girbin amfanin gona.

 

Ya yi nuni da cewa wuraren da ke da ƙarancin magudanar ruwa ko kuma waɗanda ke kusa da hanyoyin ruwa na iya zama mafi haɗari ga ambaliya.

 

Sanarwar ta shawarci manoman da su daina amfani da takin zamani domin gujewa wankewa da almubazzaranci, da kuma girbi manyan amfanin gona da wuri domin hana lalacewa daga ruwan sama.

 

Yana ƙarfafa manoma da su ɗauki hasashen da gaske kuma su hanzarta yin aiki don rage cikas da kiyaye rayuwarsu.

 

REL/ALI MUHAMMAD RABIU

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa ta horas da malamai 20,000 fasahar sadarwar zamani
  • INEC Ta Gudanar da Taron Masu Ruwa da Tsaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi na Babura/Garki
  • Majalisar Kasa Na Duba yiwuwar Dawo Da Gwamnan Jihar Rivers Fabura Kafin Cikar Wa’adin Watanni Shida.
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Tallafin Miliyoyin Naira Ga Ƴan NURTW da Mahauta a Jigawa
  • Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5
  • Manyan makarantu 2 ne kacal ke da rajista a Katsina — Gwamnati
  • An shawarci Manoman Kwara Da Su Yi Taka-Tsan-Tsan Saboda Hasashen Ruwa Da Tsawa A Jihar
  • An Kaddamar da Makon MNCH na 2025, Ya Rarraba Fakitin Bayarwa 6,000, Kayan C/S 500
  • Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana
  • Ma’aikatar Leken Asirin JMI Ta Ce Ta Gano Shirin Kashe Manyan Mutane 35 a kasar