Gwamna Mohammed Umar Bago na jihar Neja ya bayyana cewa gwamnatin jihar na hada rijistar manoma da masu rike da mukaman siyasa a cikin shirinta na inshorar lafiya domin tabbatar da ayyukan kiwon lafiya ga daukacin ‘yan kasa.

 

Gwamnan ya bayyana haka ne a Minna, a lokacin da ya karbi bakuncin abokan hulda na ci gaba daga kungiyar Global Alliance for Vaccine Immunisation GAVI, UNICEF da WHO da suka je jihar domin bikin rufe taron GAVI da ke tallafawa tsarin karfafa tsarin PHC a jihar Neja.

 

Umar Bago ya ce manoma da masu rike da mukaman siyasa da makiyaya za a yi musu rajista ta ma’aikatar makiyaya sannan ya nuna cewa duk ma’aikatan gwamnati da masu rike da mukaman siyasa za a yi musu rajista kari akan wasu su dubu dari biyu da hamsin da suka rigaya.

 

Gwamnan ya kuma jaddada aniyar gwamnatinsa na ci gaba da yin rijistar haihuwar yara bisa manufofin shirin na UNICEF.

 

Sai dai ya bayyana cewa nan da watanni 6 ne za a kaddamar da shirin samar da allurar riga-kafi, domin ba da damar samar da magunguna na zamani zuwa yankunan masu nisa da lungunan jihar.

 

Shugaban Hukumar Kula da Yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF, Ibrahim Sesay ya bayyana shirin rajistar haihuwa a matsayin na asali ga kowane yaro wanda shine dalilin da ya sa aka samu rijistar haihuwa dari bisa dari a shekarar 2024 tare da yiwa yara sama da 400,000 ‘yan kasa da shekaru 5 rijista.

 

Shugaban hukumar UNICEF a Najeriya Dr. Shyam Pathak ya yarda cewa shirin na shekaru 3 a jihar ya taimaka matuka wajen rage mace-mace da cututtuka ciki har da inganta samar da ayyukan kiwon lafiya ga marasa galihu.

 

Muhimman abubuwan da suka faru a wajen taron sun hada da bayar da lambar yabo ta UNICEF ga Gwamna Mohammed Umar Bago saboda gudunmawar da ya bayar a fannin kiwon lafiya.

 

KARSHEN ALIYU LAWAL/Wababe

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Inshora

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna

Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya yabawa Hukumar Makarantun Kimiyya da Fasaha ta Jiha bisa ƙirƙirar Kyautar Malami Mafi Nagarta, yana mai bayyana hakan da ɗaya daga cikin manyan manufofin da za su ƙarfafa koyo da koyarwa a fadin jihar.

A cikin wata sanarwa da Babban Jami’in Yaɗa Labaran sa, Hamisu Mohammed Gumel, ya fitar, gwamnan ya bayyana cewa bikin na farko na bada lambar yabo da aka gudanar a Dutse ya dace domin girmama malamai da suka yi fice ta hanyar jajircewa da sadaukar da kai.

Ya ƙara da cewa wannan mataki zai ƙara kwarin gwiwa, ya samar da gasa mai kyau, tare da inganta darussa a makarantu.

Namadi ya jaddada cewa ingancin ilimi bai tsaya kan gina makarantu kawai ba, yana ta’allaka ne ga ingancin malamai, kayan koyarwa da kuma yanayin makarantu.

Ya bayyana cewa gwamnatinsa ta fara ɗaukar malamai tare da horas da su akai-akai domin rage cunkoson ɗalibai da malamai da kuma horar da su sabbin dabarun koyarwa.

“Wannan shiri ɗaya ne daga cikin mafi kyawu da muka gani. Idan wani ya yi kuskure, sai a hukunta shi, yayin da duk wanda ya yi fice, wajibi ne a yaba masa. Wannan shi ne yadda ake samun cigaba,” in ji gwamnan.

Ya bukaci sauran hukumomin ilimi kamar Hukumar Gudanar da Makarantun Sakandare, Hukumar Ilimin Addinin Musulunci, da Ma’aikatar Ilimin Firamare su yi koyi da wannan tsari domin ƙara ƙarfafa gwanintar malamai a dukkan matakai.

Gwamnan ya kuma sake jaddada  cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da maida hankali wajen gina makarantu, horar da malamai, da walwalar su.

Ya tabbatar da cewa za a ci gaba da baiwa bangaren ilimi goyon baya don inganta sakamakon koyo a makarantu a fadin Jihar Jigawa.

 

Usman Muhammad Zaria 

 

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • UNICEF Ya Ba Da Tallafin Kayayyakin Aiki Ga Cibiyoyin Lafiya A Kirikasamma
  • Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban
  • Tinubu ya janye dokar ta-ɓaci da ya sanya a Ribas
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
  • ’Yan sanda sun sasanta rikicin asibitin AKTH da KEDCO
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa