Gwamna Mohammed Umar Bago na jihar Neja ya bayyana cewa gwamnatin jihar na hada rijistar manoma da masu rike da mukaman siyasa a cikin shirinta na inshorar lafiya domin tabbatar da ayyukan kiwon lafiya ga daukacin ‘yan kasa.

 

Gwamnan ya bayyana haka ne a Minna, a lokacin da ya karbi bakuncin abokan hulda na ci gaba daga kungiyar Global Alliance for Vaccine Immunisation GAVI, UNICEF da WHO da suka je jihar domin bikin rufe taron GAVI da ke tallafawa tsarin karfafa tsarin PHC a jihar Neja.

 

Umar Bago ya ce manoma da masu rike da mukaman siyasa da makiyaya za a yi musu rajista ta ma’aikatar makiyaya sannan ya nuna cewa duk ma’aikatan gwamnati da masu rike da mukaman siyasa za a yi musu rajista kari akan wasu su dubu dari biyu da hamsin da suka rigaya.

 

Gwamnan ya kuma jaddada aniyar gwamnatinsa na ci gaba da yin rijistar haihuwar yara bisa manufofin shirin na UNICEF.

 

Sai dai ya bayyana cewa nan da watanni 6 ne za a kaddamar da shirin samar da allurar riga-kafi, domin ba da damar samar da magunguna na zamani zuwa yankunan masu nisa da lungunan jihar.

 

Shugaban Hukumar Kula da Yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF, Ibrahim Sesay ya bayyana shirin rajistar haihuwa a matsayin na asali ga kowane yaro wanda shine dalilin da ya sa aka samu rijistar haihuwa dari bisa dari a shekarar 2024 tare da yiwa yara sama da 400,000 ‘yan kasa da shekaru 5 rijista.

 

Shugaban hukumar UNICEF a Najeriya Dr. Shyam Pathak ya yarda cewa shirin na shekaru 3 a jihar ya taimaka matuka wajen rage mace-mace da cututtuka ciki har da inganta samar da ayyukan kiwon lafiya ga marasa galihu.

 

Muhimman abubuwan da suka faru a wajen taron sun hada da bayar da lambar yabo ta UNICEF ga Gwamna Mohammed Umar Bago saboda gudunmawar da ya bayar a fannin kiwon lafiya.

 

KARSHEN ALIYU LAWAL/Wababe

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Inshora

এছাড়াও পড়ুন:

Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin Tarayya ta roƙi ƙasashen Isra’ila da Iran da su daina rikici, su zauna lafiya su sasanta tsakaninsu. 

A wata sanarwa da Ma’aikatar Harkokin Waje ta fitar, ta bayyana damuwa kan yadda rikicin ke ƙara ta’azzara, inda ta nemi ɓangarorin biyu da su kai zuciya nesa don samar da zaman lafiya a duniya baki ɗaya.

Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai Mulkin Tinubu ya fi kowane muni tun bayan dawowar mulkin farar hula — Dalung

Sanarwar ta ce faɗa da ramuwar gayya na jefa rayukan fararen hula cikin hatsari, kuma yana iya haddasa rikici mai muni a yankin Gabas ta Tsakiya, wanda hakan zai iya barazana ga tsaron duniya da kuma ci gaban tattalin arziƙi dunuya.

“Mu a matsayimmu na ƙasa mai son zaman lafiya, muna roƙon ƙasashen da ke rikici da su zauna su tattauna maimakon su ci gaba da faɗa.”

Gwamnatin Tarayya ta kuma yi kira ga ƙasashen duniya, musamman Kwamitin Tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya, da su ɗauki matakai don hana yaɗuwar rikicin da kuma samo hanyar warware matsalar.

Sanarwar ta ƙara da cewa amfani da ƙarfin soji ba shi da amfani matuƙa, domin faɗa ba zai kawo sauƙi ba.

Najeriya ta ce a shirye ta ke ta bayar da taimako domin hana yaɗuwar rikicin da kuma tabbatar da zaman lafiya a yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAF Na Shirin Siyo Jiragen Yaki Masu Saukar Ungulu Daga Amurka
  • Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikacin Jami’ar Northwest a Kano
  • Za A Watsa Shirin “Bayanan Magabata Dake Jan Hankalin Xi Jinping” A Kafofin Watsa Shirye-shiryen Kasashen Tsakiyar Asiya Biyar
  • Isra’ila da Iran su daidaita rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu
  • Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi
  • Gwamnatin Bauchi Ta Fara Shirin Kirkirar Sabbin Masarautu Da Sarakuna Da Gundumomi
  • Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina
  • NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya