Za a Kashe Sama da Naira Biliyan 9 Wajen Gyran Asibitoci a Jigawa
Published: 28th, January 2025 GMT
A cim ma burin Gwamna Umar Namadi na ci gaban bil’adama a cikin ajandar mai dauke da abubuwa 12, majalisar zartaswar jihar Jigawa ta kafa wani kwamiti mai mambobi 10 domin samar da hanyoyin da za a bi wajen nemo masu hazaka domin karfafa kirkire-kirkire a tsakanin matasa masu tasowa a jihar.
Kwamishinan yada labarai, matasa, wasanni da al’adu na jiha Alhaji Sagir Musa Ahmed ya bayyana haka bayan taron majalisar da aka gudanar a Dutse.
Ya ce, kwamitin ya kunshi kwamishinonin lafiya, muhalli, kananan hukumomi yayin da kwamishinan ilimi mai zurfi zai zama shugaba.
Sauran mambobin sun hada da masu ba da shawara kan fasaha, ICT da tattalin arziki na dijital, ilimi mai zurfi, aikin gona, babban darakta na hukumar karfafa matasa da samar da aikin yi da kuma babban sakatare mai zaman kansa na gwamna.
Sagir Musa Ahmed ya ce, mai ba da shawara na musamman kan fasaha da kirkire-kirkire ne zai zama sakataren kwamitin.
Hakazalika majalisar ta ware wa kwamitin makonni 2 domin gabatar da rahotonsa.
Ya kara da cewa, matakin majalisar na da burin bunkasa al’adun kirkire-kirkire, kirkire-kirkire da kasuwanci a tsakanin ‘yan jihar musamman matasa kamar yadda ma’aikatar ilimi mai zurfi ta gabatar.
Ya kuma bayyana cewa, majalisar ta amince da kaddamar da wani shiri na musamman na wayar da kan jama’a a matsayin “Gwamnati da Jama’a” a karkashin jagorancin Gwamna Malam Umar Namadi.
A cewarsa, za a kaddamar da shirin ne a dukkanin kananan hukumomin 27 da za a sanar da taron majalisar al’umma a kowace karamar hukumar domin tattaunawa kai tsaye da Gwamna da sauran jami’an gwamnati.
Ya yi nuni da cewa, gaba daya babban burin shi ne tabbatar da cewa al’ummar jihar ba wai kawai masu cin gajiyar ayyuka da shirye-shiryen gwamnati ba ne, har ma sun kasance masu taka rawar gani wajen tsara makomarsu da kuma sanin ayyukan da gwamnatin jihar ke ci gaba da gudanarwa da kuma shirye-shiryenta.
Kwamishinan ya ce majalisar zartaswar jihar ta amince da sake farfado da cibiyoyin kiwon lafiya matakin farko guda 114 a fadin jihar.
Ya ce majalisar ta amince da sama da Naira Biliyan 9.7 don farfado da PHC a fadin kananan hukumomi 27 da ke jihar a karkashin gwamnatin.
KARSHE/USMAN MZ/Wababe
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Shirya Fara Tantance ‘Yan Fansho
Hukumar Fensho ta Jihar Jigawa da Kananan Hukumomin jihar ta shirya fara aikin tantance ‘yan fansho da ke cikin tsarin.
Shugaban Ma’aikatan Gwamnatin Jihar, Alhaji Muhammad K. Dagaceri ne ya bayyana haka yayin wani taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a Gidan Fansho, inda shugabannin kungiyar ‘Yan Fansho ta Najeriya reshen Jigawa suka halarta.
A cewarsa, an shirya fara aikin tantancewar ne daga ranar Litinin, 5 ga Mayu, 2025.
Alhaji Dagaceri ya bayyana cewa, an shirya hakan ne da nufin sabunta tsarin biyan fansho tare da tabbatar da ingancin bayanai.
Ya ce, aikin tantancewar zai gyara wasu ‘yan kura-kurai da suka kunno kai a cikin shekaru uku da suka gabata, da kuma tabbatar da ingantattun bayanai a jadawalin biyan fansho.
Ya kara da cewa, wannan yunkuri ya yi daidai da kudirin jihar gwamnati na tabbatar da gaskiya da rikon amana a harkokin mulki, tare da bai wa ‘yan fansho dama su gyara duk wani bayanin da bai cika ba a takardunsu.
Shi ma da ya ke jawabi, Akanta Janar na Jihar, Alhaji Abdullahi S.G. Shehu, ya jaddada cewa aikin tantancewar zai bai wa ‘yan fansho damar sabunta bayanansu da suka bace ko suka canza a takardunsu.
Saboda haka, ya bukaci dukkan ‘yan fansho daga ma’aikatun gwamnati, sassan hukumomi, kananan hukumomi da kuma hukumomin ilimi na kananan hukumomi da su halarci tantancewar a ranar da aka tsara kamar yadda yake cikin jadawalin aikin.
A jawabinsa, Shugaban kungiyar kananan hukumomi ALGON ta Jihar Jigawa, Farfesa Salim Abdurrahman, ya tabbatar da cikakken goyon baya daga shugabannin kananan hukumomi 27 domin cimma burin aikin.
Shugaban na ALGON wanda shugaban karamar hukumar Malam Madori, Alhaji Salisu Sani ya wakilta, ya bukaci ‘yan fanshon da su ba da cikakken haɗin kai don samun nasarar shirin.
Shi ma Shugaban hukumar, Dr. Bilyaminu Shitu Aminu, ya bukaci ‘yan fansho daga sassa daban-daban da su ba da hadin kai domin cimma burin da aka sanya, tare da jaddada cewa su ziyarci sakatariyar kananan hukumominsu domin a tantance su.
Shugaban Kungiyar ‘Yan Fansho ta Najeriya reshen Jihar Jigawa, Alhaji Umar Sani Babura, ya yi alkawarin cewa kungiyar za ta bada cikakken goyon baya domin nasarar wannan shiri.
Dukkan ‘yan fansho daga Ma’aikatun Gwamnati, Kananan Hukumomi, da Hukumomin Ilimi na Kananan Hukumomi da ke cikin tsarin fanshon, ya zama wajibi su halarci wannan tantancewa a ranakun da aka tsara a jadawalin aikin.
Usman Muhammad Zaria