HausaTv:
2025-07-31@08:12:23 GMT

Ana Bikin Zagayowar Ranar Aiko Da Manzon Tsira (SAW)

Published: 28th, January 2025 GMT

Yau Talata ana bikin tunawa da aiko ma’aiki tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalan gidansa wato Yaumil Mab’as.

Ranar Mab’as 27 Ga Rajab rana ce ta murna da farin ciki saboda saukar Mala’ika Jibril (a.s) a kogon Hira dauke da sakon ayoyin farko na Kur’ani zuwa ga (Annabi) Muhammad ibn Abdullah (s.

a.w) a lokacin yana dan shekara 40.

Babbar manufar gudanar da wannan biki ita ce tunawa da ranar aiko manzon Allah Nuhammad (SAW), wanda ya zo wa dan adam da sako tsira daga halaka da kuma fita daga duhun kafirci da jahilci.

Manzon Allah (SAW) ya kasance mutum na musamman a cikin larabawa, wanda dukkanin al’ummar da ke tare da shi ta yi masa shedar gaskiya da rikon amana da karamci da kuma girmama jama’a, wadanda suka girme shi da ma wadanda ya girma.

Allah madaukain sarki ya aiko da sako zuwa ga bil adama, wanda ya zama sanadin shiririyar jama’a da dama a lokacinsa, mafi yawan wadanda suka muslunta tare da manzon Allah a Makka sun musulunta ne sakamakon kyawawan dabi’unsa, kamar yadda da dama daga cikin wadanda suka muslunta a Madiana bayan hijira sun karbi muslunci ne sakamakon kyawawan dabi’u da suka gani tare da manzon Allah, wadanda addinin ke koyar da dan Adam.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban hukumar zabe ta jihar Bauchi ya rasu

Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta jihar Bauchi (BASIEC), Ahmed Makama Hardawa, ya rasu.

Marigayin ya rasu ne ranar Talata a Abuja, bayan ya yi fama da gajeruwar jinya.

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed ne ya tabbatar da rasuwarsa a cikin wata sanarwa ranar Laraba.

Muna tafe da karin bayani…

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 
  • Shugaban hukumar zabe ta jihar Bauchi ya rasu
  • Shugaban SUBEB Yayi Alkawarin Bayar Da Tallafin Ilimi A Jihar Nasarawa
  • Shugaban Ivory Coast Ouattara zai sake takara wa’adi na huɗu
  • Remi Tinubu ta bai wa waɗanda harin Benuwe ya shafa tallafin Naira biliyan ɗaya
  • Remi Tinubu ta ba da tallafin Naira biliyan ɗaya ga waɗanda harin Benuwe ya shafa
  • Kasar Faransa Ta Yi Allah Wadai Da Harin Ta’addancin Da Aka Kai Birnin Zahedan Na Kasar Iran
  • Gwamna Namadi Ya Biya Sama Da Naira Biliyan Daya Ga Tsofaffin Ma’aikata
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan Almujtaba 121
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan Almutaba (a) 120