Masu zanga-zanga sun ƙone matar tsohon Firaministan Nepal
Published: 10th, September 2025 GMT
Rabi Laxmi Chitrakar, matar tsohon Firaministan Nepal, Jhalanath Khanal, ta rasu bayan masu zanga-zanga sun cinna wa gidansu da ke unguwar Dallu, Kathmandu wuta.
Majiyoyi sun ce masu zanga-zangar sun rufe ta a cikin gidan kafin daga baya suka cinna wa gidan wuta.
An harbe ’yan sanda 3 har lahira a Kogi Babban layin wutar lantarki ya sake lalacewaAn kai ta Asibitin Kirtipur Burn Hospital amma ta rasu, saboda raunukan da ta samu.
Wannan lamari ya faru ne biyo bayan wata zanga-zanga da matasa suka fara a Nepal.
Masu zanga-zangar suna neman a sallami jami’an gwamnati saboda zargin cin hanci, nuna son kai, da matsalolin da suka shafi tattalin arziƙi.
Aƙalla mutum 22 ne suka rasu tun daga ranar Litinin, yayin da sama da 300 suka ji jikkata.
Ƙungiyar kara haƙƙin ɗan Adam ta Amnesty International, ta ce ’yan sandan Nepal sun yi amfani da harsasan gaske wajen tarwatsa masu zanga-zangar.
Wasu bidiyo da aka yaɗa sun nuna yadda aka dinga jefa abubuwa masu fashewa a gidajen manyan ‘yan siyasa, ciki har da tsofaffin Firaminista K.P. Sharma Oli, Sher Bahadur Deuba, da Pushpa Kamal Dahal.
An kuma kai wasu gine-ginen gwamnati hari, ciki har da babban ofishin gudanarwa da fadar shugaban ƙasa.
Sakamakon tashin hankali, Firaministan Nepal, Oli, mai shekaru 73, ya yi murabus don taimaka wa wajen samo mafita ta siyasa.
Wasu ministoci, ciki har da masu kula da harkokin ruwa, noma, da harkokin cikin gida, su ma sun yi murabus.
Al’amura sun rikice a ƙasar, yayin da hukumomi ke ƙoƙarin wanzar da doka da oda, tare da kira a kwantar da hankali da tattaunawa don kawo ƙarshen lamarin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Matar Tsohon Firaminista
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
Gwamnatin mamayar Isra’ila ta yanke hukuncin kisa kan masu fama da cutar kansa da kuma waɗanda suke fama da matsalar koda na mutuwa a Gaza domin hana fitar da su wata kasa don neman magani
Cibiyar Kare Hakkin Dan Adam ta Gaza ta bayyana matukar damuwarta game da tabarbarewar lafiyar marasa lafiya da ke fama da cutar kansa da kuma cutar koda a Zirin Gaza. Wadannan cututtuka sun kara ta’azzara ne sakamakon hare-haren sojojin mamayar Isra’ila kan Gaza da kuma ci gaba da killace yankin bayan tsagaita bude wuta, gami da hana shigar dq magunguna da kayayyakin ayyukan likitanci masu muhimmanci cikin yankin. Cibiyar ta kuma yi nuni da tsauraran matakan fitar da marasa lafiya zuwa ƙasashen waje don neman magani.
A cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Lahadi, Cibiyar ta tabbatar da cewa, wannan yanayin ba shi da wata shakka cewa Isra’ila na aiwatar da manufar kisan gilla a kan dubban marasa lafiya ta hanyar hana su ‘yancinsu na rayuwa da magani da gangan, da kuma canza wahalarsu zuwa wani nau’in hukunci na gama gari.
Cibiyar ta ambaci majiyoyin lafiya da ke tabbatar da cewa, akwai marasa lafiya 12,500 da ke fama da cutar kansa a Zirin Gaza, ciki har da ƙananan yara. Ta lura cewa mata sun kai kusan kashi 52% na dukkan masu cutar kansa a Gaza.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kasar Qatar Ta Ba Da Tallafin Gaggawa Ga Al’ummar Sudan Bayan Gumurzun El-Fasher November 2, 2025 IAEA : Babu wata shaida da ke nuna cewa Iran na kera makaman nukiliya November 2, 2025 Amurka : zamu dauki matakin soja idan Najeriya ta gaza kawo karshen kashe Kiristoci November 2, 2025 Hamas ta musanta zargin Amurka na cewa tana sace kayan agaji a Gaza November 2, 2025 Wasu Yan Ta’adda Sun Kashe Dakarun Sa Kai 2 A Kudu Maso Gabashin Iran November 2, 2025 Sojojin Amurka Na Kara Fuskantar Venezuwela Adaidai Lokacin da Trump Ke Musanta Batun Kai Hari November 2, 2025 Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon November 2, 2025 Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya November 2, 2025 Shugaban AmurkaTrump ya yi barazanar daukar matakin soji kan Najeriya November 2, 2025 Kamaru: Jagroan ‘Yan Hamayya Ya Yi Kira Da A Tsayar Da Harkoki A Fadin kasar November 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci