Leadership News Hausa:
2025-11-03@03:06:22 GMT

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

Published: 5th, September 2025 GMT

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

“Tun daga ranar farko, na gaya wa abokan aikina da ke cikin jam’iyyar PDP cewa kuna daba wa cikinku wuka. Idan kuka bari abubuwan da ke faruwa su ci gaba a haka, za ji a jikinku. Kuma me na ce? Ba za ku iya fitar da dan takarar shugaban kasa da shugaban jam’iyya na kasa su fito a yankin guda ba,” in ji Wike.

 

Tsohon gwamnan Jihar Ribas ya zargi PDP da rashin yin adalci wajen rarraba mukamai da kuma watsi da kiraye-kirayen yin adalci da daidaito, a cewarsa, wannan mataki su ne makasudin rashin nasarar jam’iyyar a zaben bara.

 

“Yana da kyau tun yanzu a warwaren matsalar tikitin takarar shugaban kasa kuma na shugaban jam’iyyar na kasa n. A gani na hakan shi ya fi dacewa. Kuma shi ne adalci a siyasance. Ba na yin dana sani a kan haka,” ya bayyana.

 

Wike ya jaddada cewa dole ne shugabancin kasar nan ya sake komawa yankin kudu don tabbatar da adalci da daidaito a cikin harkokin siyasar Nijeriya.

 

A cewarsa, girman kai da kin sauraron gaskiya daga wasu shugabannin PDP sun sa jam’iyyar taraunata, sannan kuma ta samu rashin karfi tare rasa samun mulki.

 

Ya kuma musanta maganganun da suka shafi yiwuwar dawowar Obi cikin PDP, yana bayyana wannan mataki a matsayin mai tsananin hadari a cikin jam’iyyar.

 

“Ta wani dalili za ku dawo mana da Obi cikin wannan jam’iyyar? Kana son kashe jam’iyyar ne? Obi wanda yake zagin jam’iyyar, yana cewa ta lalace, yanzu kuma jam’iyyar ta zama mai kyau a gare shi ne? Burin mutum na iya sa mutane su kasance har zuwa gidan Shaidan,” in ji Wike.

Ministan ya kara jaddada cewa irin wannan hukunci zai kara lalata ingancin jam’iyyar kuma zai tarwatsa duk wata ginshikin da ya rage a cikin jam’iyyar a halin yanzu.

Ya ce, “Idan kana son tarwatsa jam’iyyar ne, to zai ka gaggauta shigo da Obi cikin jam’iyyar. Babu wata hanya da zai dawo saboda burinsa na kashin kai. Babu dabara da kuma ka’ida a wannan mataki,” ya kara bayyanawa.

Wike ya ci gaba da cewa yana tsaye kan matsayinsa cewa a yi adalci da gaskiya da kuma bin tsarin karba-karba domin ta wannan hanya ce kadai jam’iyyar PDP za ta sau damar dawo da tasirinta a kasar nan.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: cikin jam iyyar

এছাড়াও পড়ুন:

Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa

Tsohuwar jarumar Kannywood, Mansurah Isa, ta ƙaryata labarin da wata jaridar intanet ta yaɗa cewa wai tana son ta auri shahararren dan TikTok, Ashiru Mai Wushirya, wanda ya yi tashe a kafafen sada zumunta a ’yan kwanakin nan.

A wani saƙo da ta wallafa, Mansurah ta ce labarin ƙarya ne kuma ya jefa ta da iyalinta cikin ruɗani da damuwa.

Ta ce, “Na shiga firgici bayan na ga wannan labarin. Ba ni da wata alaka da Mai Wushirya. Wannan sharri ne tsagwaron karya.”

Rahoton da aka yada a jaridar AMC Hausa ya yi iƙirarin cewa wai Mansurah ta ce ta shirya auren Mai Wushirya idan har yana son ta da gaske.

Kofin kofi mafi tsada a duniya ya shiga kasuwa a kan Naira miliyan 1.5m An yi garkuwa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Kebbi

Amma jarumar ta yi watsi da wannan iƙirarin, tana mai cewa jaridar ta ɓata mata suna kuma ta karya ƙa’idojin aikin jarida.

Ta ce, “Na kira su, na ba su awa 24 su sauke labarin, amma har yanzu ba su yi hakan ba. Sun kira ni sun ba ni hakuri a waya, amma labarin har yanzu yana nan. Wannan abu ya zubar min da mutunci kuma ya saka iyalina cikin tashin hankali,” ina ji ta.

Mansurah ta bayyana cewa yanzu tana cikin shirin ‘WalkAwayCancer’, wani gagarumin shiri na wayar da kan jama’a kan mcutar daji, amma wannan labarin karya ya yi ƙoƙarin karkatar da hankalin mutane daga ainihin aikinta.

“Kun hana ni barci da kwanciyar hankali saboda labarin da babu gaskiya a cikinsa. Amma in sha Allahu, za ku ji daga gare mu,” in ji ta cikin fushi.

Har zuwa lokacin da muka kammala wannan labarin dai, kamfanin AMC Hausa bai fitar da wata sanarwa ba dangane da ƙarar da Mansurah ke shirin kai musu bisa zargin yaɗa labarin ƙarya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Rikicin PDP: Tsagin Wike ya dakatar da Damagum
  • PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu ’yan tsagin Wike
  • PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu da ke da alaƙa da Wike
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa
  • Dan Majalisar Jema’a/Sanga, Daniel Amos, Ya Koma Jam’iyyar APC
  • Za mu ci gaba da shirye-shiryen babban taronmu — PDP
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar