Leadership News Hausa:
2025-09-18@00:44:32 GMT

Gwamnatin Kaduna Ta Zargi El-Rufai Da Yunkurin Tayar Da Tarzoma A Jihar

Published: 5th, September 2025 GMT

Gwamnatin Kaduna Ta Zargi El-Rufai Da Yunkurin Tayar Da Tarzoma A Jihar

Dr. Shuaibu ya ce maganganun El-Rufai na baya-bayan nan, ciki har da zargin da ya yi a talabijin na kasa cewa gwamnati ta tarayya da ta jihar na “ba wa ‘yan ta’adda cin hanci,” karya ne, mai hadari, kuma an yi su ne don raunana kokarin tsaro. Ya kara da cewa Ofishin Mai Ba Shugaban Kasa Shawara kan Harkokin Tsaron (ONSA) ya riga ya musanta wannan zargi a matsayin mara tushe.

 

Ya ce hukumomin tsaro da shirye-shiryen cikin gida sun samu nasarori masu yawa a karkashin gwamna Uba Sani, inda ya bayar da misalin cafke manyan shugabannin ‘yan ta’adda da kuma dawo da kwanciyar hankali a yankunan da ke cikin tashin hankali kamar Birnin Gwari, Giwa, Kajuru da Kachia.

 

Kwamishinan ya kara da zargin cewa El-Rufai ya kara kokarin yin tasiri bayan kalubalen siyasa da abokan siyasa na suka fuskanta a yayin zaben cike gurbi na 16 ga Agusta. Ya kuma bayyana cewa gwamnatin Gwamna Sani ta mai da hankali kan gina zaman lafiya, hadin kai da ci gaba, kuma ba za ta bar kowanne mutum ya “kawo koma-baya ga ci gaban da aka samu” ba. A daya bangaren kuma Kungiyar Kwararrun ‘Yan APC (ALP) ta nuna rashin jin dadi kan maganganun da ake danganta wa tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Mallam Nasir El-Rufai, inda ya yi zargin cewa gwamnatin tarayya karkashin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na kara wa ‘yan ta’adda karfi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi

Hukumomin a Ƙasar Saudiyya, sun saki wasu ’yan Najeriya uku da aka kama a Jeddah kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi.

Waɗanda aka saki sun haɗa da Hajiya Maryam Hussain Abdullahi, Hajiya Abdullahi Bahijja Aminu, da Malam Abdulhamid Saddieq.

Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano

Sun shafe makonni huɗu a tsare kafin aka tabbatar da cewa ba su da laifi.

A wajen taron manema labarai a Abuja, mai magana da yawun Hukumar Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi (NDLEA), Femi Babafemi, ya ce sakin ya biyo bayan tttaunawa da Shugaban NDLEA, Janar Mohamed Buba Marwa (mai ritaya), tare da Hukumar Hana Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Saudiyya.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ne, ya bayar da cikakken goyon baya wajen ganin an saki waɗanda aka kama.

Bincike ya gano cewa wasu masu safarar miyagun ƙwayoyi ne a Filin Jirgin Sama na Mallam Aminu Kano, suka ƙwayoyin a jakunkuna waɗanda aka kama.

Mutanen uku da aka kama, sun tashi a jirgin Ethiopian Airlines a ranar 6 ga watan Agusta don yin Umara, amma aka kama su a Saudiyya.

Binciken NDLEA ya kai ga kama wani shugaban masu safarar miyagun ƙwayoyin, mai shekaru 55, Mohammed Ali Abubakar (wanda aka fi sani da Bello Karama).

Hakazalika, hukumar ta kama wasu mutum uku ciki har da ma’aikatan jirgi.

Mutanen da aka kama su ne suka shirya safarar ƙwayoyin a jakunkunan mutane da aka kama a Saudiyya.

NDLEA ta gabatar da shaidun da suka tabbatar da cewa mutanen da aka kama a Saudiyya ba su da laifi.

Sakamakon haka, hukumomin Saudiyya suka sako ɗaya daga cikinsu a ranar 14 ga watan Satumba, sannan suka sako sauran biyun a ranar 15 ga watan Satumba.

Babafemi, ya ce Marwa ya gode wa hukumomin Saudiyya saboda mutunta yarjejeniyar haɗin kai tsakaninsu da Najeriya.

Ya kuma gode wa Shugaba Tinubu da sauran manyan jami’an gwamnati, ciki har da Ministan Shari’a, Ministan Harkokin Ƙasashen Waje, Ministan Sufurin Jiragen Sama, da Mai Bai Wa Shugaba Shawara Kan Harkar Tsaro, saboda gudummuwarsu.

Ya ƙara da cewa wannan lamari ya nuna cewa Najeriya tana tsayawa wajen kare ‘yan ƙasarta a ƙasashen waje kuma ba za ta yadda wani ɗan Najeriya ya sha wahala saboda laifin da bai aikata ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • Kwamitin bincike na MDD ya zargi Isra’ila da aikata “kisan kare dangi” a Gaza
  • Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
  • Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja