Aminiya:
2025-11-03@01:26:57 GMT

Girgizar ƙasa ta hallaka fiye da mutum 800 a Afghanistan

Published: 2nd, September 2025 GMT

Mutum sama da 800 sun mutu, yayin da wasu fiye da 2,500 suka jikkata sakamakon girgizar ƙasa mai ƙarfin maki 6 da ta auku a lardin Kunar da ke gabashin Afghanistan, kusa da iyakar Pakistan.

Girgizar ƙasar wadda ta auku da misalin ƙarfe 12 na daren Lahadi ta rusa gidaje da dama da aka gina da laka da duwatsu, lamarin da ya sanya dubban mazauna kwana a waje.

Manchester United za ta ɗauki golan Antwerp, Senne Lammens An kama uba da ɗansa kan yi wa ’yar shekara 13 fyaɗe a Gombe

Rahotanni sun ce yara da mata na daga cikin waɗanda suka rasa rayukansu, kuma tuni an yi jana’izarsu.

Mai magana da yawun gwamnatin Taliban, Zabihullah Mujahid, ya bayyana fargabar cewa adadin waɗanda suka mutu ko jikkata na iya ƙaruwa domin akwai da dama da suka maƙale a ƙarƙashin baraguzan gine-gine.

Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana cewa wasu ƙauyukan da abin ya fi shafa ba za a iya kai musu agaji ba saboda hanyoyin da suka toshe.

Shugaban MDD, Antonio Guterres, ya miƙa ta’aziyarsa ga al’ummar Afghanistan cikin wata sanarwa da ya ce “ina goyon bayan da ƙara wa al’ummar Afghanistan ƙwarin gwiwa a wannan lokaci mai tsanani.”

Shi ma shugaban cocin Katolika na Vatican, Fafaroma Leo XIV, ya bayyana a wata sanarwa cewa ya “yana matuƙar baƙin ciki da rayukan da suka salwanta a sakamakon girgizar ƙasar da ta auku a gabashin Afghanistan.”

A daren nan ne, ƙungiyoyin ƙwallon ƙafa na Afghanistan da UAE suka yi shiru na minti ɗaya domin girmama waɗanda suka rasa rayukansu, kafin fara wasan ƙetaren ƙasa a Sharjah.

Girgizar ƙasar ba ita farau ba

Afghanistan dai na cikin ƙasashen da ke yawan fuskantar girgizar ƙasa, musamman a yankin tsaunukan Hindu Kush.

Tun daga shekarar 1900, an samu girgizar ƙasa guda 12 da ƙarfinta ya haura maki 7 a yankin arewa maso gabas na ƙasar, a cewar Brian Baptie, wani masani a Birtaniya.

“Wannan irin girgiza, haɗe da haɗarin bala’o’i da kuma irin ginin da ke yankin, na iya haddasa asarar rayuka masu yawa,” in ji shi.

A watan Oktoba na 2023, girgizar ƙasa mai ƙarfin maki 6.3 ta girgiza lardin Herat da ke yammacin ƙasar, inda mutane sama da 1,500 suka mutu, kuma gidaje sama da 63,000 suka lalace ko rushe.

A watan Yuni na 2022, girgizar ƙasa mai ƙarfin maki 5.9 da ta auku a lardin Paktika, an rasa rayuka fiye da 1,000 kuma dubban mutane suka rasa matsuguni.

Bayan shafe shekaru 40 tana yaƙi, Afghanistan na fuskantar manyan ƙalubalen jin ƙai.

Tun bayan dawowar Taliban a shekarar 2021, tallafin ƙasashen waje ya ragu sosai, lamarin da ya sa ƙasar ke samun cikas wajen ɗaukar matakan gaggawa idan bala’i ya auku.

A halin yanzu dai Afghanistan na daga cikin ƙasashe mafi talauci a duniya, tana fama da mummunan rikicin jin ƙai, yayin da dubban ‘yan Afghanistan da aka mayar daga Pakistan da Iran suka koma gida cikin wannan shekara.

Kimanin kashi 85 cikin ɗari na al’ummar Afghanistan na rayuwa da ƙasa da dala ɗaya a rana, a cewar Hukumar Raya Kasashe ta Majalisar Dinkin Duniya (UNDP).

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Girgizar ƙasa girgizar ƙasa

এছাড়াও পড়ুন:

Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu

Shugaba Bola Tinubu ya mayar wa da Shugaban Amurka, Donald Trump martani cewa Najeriya ba ta yadda da duk wani nau’in zarafin addini.

Tinubu, ya yi wannan bayani ne bayan Trump ya sake sanya Najeriya cikin jerin ƙasashen da ake kiran “Ƙasashen da ke da Babbar Matsala wajen ’Yancin Addini.”

PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu ’yan tsagin Wike Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa

Trump ya yi iƙirarin cewa Kiristoci a Najeriya na fuskantar barazana, amma ya sha alwashin cewa Amurka za ta kare su.

A cikin wani saƙo da ya wallafa a kafafen sada zumunta, Trump ya rubuta cewa: “Addinin Kirista yana fuskantar babbar barazana a Najeriya. Ana kashe dubban Kiristoci.”

A ranar Asabar, Tinubu ya mayar da martani ta kafar sada zumunta, inda ya ce Najeriya ƙasa ce mai dimokuraɗiyya wadda kundinta ya tabbatar da ’yancin yin addini.

“Najeriya tana da cikakken tanadi a kundinta da ya tabbatar da ’yancin yin addini,” in ji Tinubu.

“Tun daga shekarar 2023, gwamnatina na aiki tare da shugabannin Kiristoci da Musulmai don magance matsalolin tsaro da ke shafar jama’a daga kowane ɓangare da addini.”

Ya ƙara da cewa, kiran Najeriya ƙasa mai matsala wajen gudanar addini ba gaskiya ba ne.

“Za mu ci gaba da kare ’yancin kowane ɗan ƙasa na yin addininsa cikin walwala. Najeriya ba ta goyon bayan zaluncin addini ko kaɗan,” in ji Tinubu.

Ya kuma ce Najeriya za ta ci gaba da haɗa kai da Amurka da sauran ƙasashe domin inganta zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin mabiya addinai daban-daban.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazanar Sa Ga Nijeriya
  • Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba
  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon barazana — Kwankwaso
  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon ba barazana ba — Kwankwaso
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini ba — Tinubu
  • Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu
  •  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • Kasashen Pakistan Da Afghanistan Sun Tsawaita Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta