Aminiya:
2025-11-02@21:10:42 GMT

Kashe mutane 5 da sace Hakimi da limamai ya fusata Sakkwatawa

Published: 1st, September 2025 GMT

’Yan gudun hijira daga sama da kauyukka 10 a Ƙaramar Hukumar Shagari ta Jihar Sakkwato sun rufe hanyar Shagari zuwa Sakkwato domin nuna fushinsu ga gwamnati kan azabar da suke sha hannun ’yan bindiga a yankinsu.

Mata da mazan sun buƙaci daukin gwamnati kan abin da ke addabar su, sun rufe babbar hanyar da ta hada jihohin Sakkwato da Kebbi da Neja.

A yayin zanga-zangar a ranar Lahadi, wani daga ƙauyen Rinaye ya shaida wa Aminiya cewa, “Rashin kulawar da gwamnati ta nuna mana ya sa muka rufe hanyar mota don janyo hankalinta da jami’an tsaro gare mu a ɗauki matakin korar mana ’yan bindigar su bar yankinmu.

“Yau (Lahadi) sun jera kwana uku kullum sai sun zo sun sace mana mutane kuma babu wasu jami’an tsaro da aka kawo mana don kare mu.”

Ya ce ’yan bindigar sun tashi ƙauyuka uku a ranar Juma’a, sun tafi na biyu dana uku a ranar Assabar da Lahadi.

“A garin Rinaye sun sace mai garinmu da duka limaman garin bayan sun kashe mutum uku sun yi garkuwa da wasu mutanen garin da ba a tantance yawansu ba, a wannan Asabar da Lahadi.

“Shekaranjiya sun shiga garin Aske dodo da Tungar Barkenda Jandutse duk waɗannan wurare babu mutane a cikinsu yanzu, sun kashe mutane biyu da yin garkuwa da wasu 15,” a cewar majiyar.

Ya ce hukumomin tsaro da gwamnati ba a abin da suka yi a yanzu, ko jaje ba a kai musu ba.

Malama Tunba mai yara biyar mata uku da maza biyu daga ƙauyen Jandutse ta ce yanzu haka ba ta san inda ’ya’yanta suke ba tun da suka gudu a ranar Assabar, a haka ta yini ba abin da ta sa a bakinta.

Tumba ta yi kira ga gwamnati ta taimaka musu da tsaro mu zauna a gidajensu cikin rufin asiri, wahalar da suke ciki ta yi yawa.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) da ta jiha SEMA sun ce sun san da zaman ’yan gudun hijirar da suka gudu kan matsalar ’yan bindiga.

Bayanin ya ce, “A Ƙaramar hukumar Shagari ɗaruruwan mutane sun bar muhallansu kan rashin tsaron da ya kunno kai a yankin suna neman ɗauki.

“Don ganin halin da ake ciki, hukumomin sun tafi rukunin gidaje 30 a ƙaramar hukumar inda mutanen suka zauna sun tuntubi hakiman mutanen daga cikinsu akwai Hakimin ‘Yan Dundaji, Malam Muhammad Bello Magaji, da Maigarin Tungar-Barke, Muhammadu Tudu, wanda ya tabbatar da harin da aka kai musu kwana uku baya, yana da ’yan gudun hijira da yawa.

Sauran ƙauyukan da abin ya shafa sun haɗa da Tungar-Barke, Lungu, Aske-Dodo, Tungar-Doruwa, Zango, ‘Yan Yandu, Tungar Na’anza, Ila, da sauransu.
A halin da ake ciki hukumomin na kira ga gwammati ta kawo ɗaukin gaggawa musamman samar da tsaro a ƙauyukan don mutanen su koma gidajensu cikin aminci.

Wakilinmu ya tuntubi shugaban karamar hukumar Shagari Honarabul Alhaji Maidawa sai dai bai samu jin ta bakinsa ba har zuwa haɗa labarin.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Madagascar Ta Sanar da Kafa Sabuwar Gwamnati Tare da Manyan ‘Yan Adawa

Madagascar ta sanar da kafa sabuwar gwamnati wadda ta kunshi fitattun ‘yan adawa guda uku a manyan mukamai na ministoci.

An gabatar da majalisar ministoci mai mambobi 29, wacce ta kunshi mata 10, a wani biki da aka gudanar a Fadar Gwamnatin Yavoloha da ke babban birnin kasar, Antananarivo.

Shugaban rikon kwarya Michael Randrianireina ya bayyana a lokacin bikin cewa manyan abubuwan da sabuwar gwamnatin ta sa gaba sun hada da yaki da rashin adalci, aiwatar da matakan tsuke bakin aljihu, da kuma samar da yanayin kasuwanci mai dorewa.

Ya kara da cewa kowane minista dole ne ya samar da sakamako mai kyau cikin watanni biyu, yana mai gargadin cewa rashin yin hakan a cikin wannan lokacin zai zama gazawa kuma zai iya haifar da maye gurbin minister a nan take.

An nada Christine Razanahasoa, tsohuwar Ministar Shari’a kuma tsohuwar Kakakin Majalisar Dokoki ta Kasa, a matsayin Ministar Harkokin Waje, kuma an nada Fanerisoua Irinavo, tsohuwar alkali wacce ta dawo daga gudun hijira daga  Faransa, a matsayin Ministar Shari’a.

An nada Hanitra Razavimanantsoa, ​​’yar majalisa daga jam’iyyar Tiaco Madagascar karkashin jagorancin tsohon shugaban kasar Marc Ravalomanana, a matsayin Ministar Kasa a ma’aikatar Sake Gina Kasa. Waɗannan mutane uku suna wakiltar muryoyin  manyan bangarorin ‘yan adawa a Madagascar.

Jagoran juyin mulkin, Michel Randrianireina, ya kwace mulki a ranar 14 ga Oktoba bayan tsohon shugaban kasar Andry Rajoelina ya tsere daga kasar a cikin jirgin saman sojojin Faransa bayan makonni na zanga-zanga.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran ta yi fatali da kalamman IAEA Kan Shirin Nukiliyarta October 30, 2025 Trump Ya Umarci Ma’aikatar Yakin Amurka Ta koma gwajin makaman nukiliya October 30, 2025 Isra’ila ta amince da fadada matsugunai a Yammacin Kogin Jordan October 30, 2025 Gaza: hare-haren Isra’ila sun kashe mutane 100 Cikin Kwanaki Biyu October 30, 2025 Sudan : Kasashen duniya na tir da cin zarafi a El-Fasher October 30, 2025 Iran Ta Jaddada Bin Hanyar Diflomasiya Ko Da A Lokacin Yaki Ne Amma Ba Zata Amince Da Bin Umarni Ba October 30, 2025 Qalibaf: Amurka Tana Yaudarar Duniya Da Zaman Lafiya, Alhalin Tana Ci Gaba Da Kai Harin Wuce Gona Da Iri October 30, 2025 Ci Gaba Da Killace Gaza Bayan Tsagaita Bude Wuta Ya Janyo Mutuwar Mutane 1000 A Yankin October 30, 2025 Kungiyar Rapid Support Forces Ta Sanar Da Kafa Kwamitin Bincike Kan Cin Zarafin Al’umma A El Fasher October 30, 2025 An Kafa Dokar Ta Baci A Darul-Salam Saboda Tarzoman Zaben Shugaban Kasa A Tanzania October 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon barazana — Kwankwaso
  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon ba barazana ba — Kwankwaso
  • Hamas ta musanta zargin Amurka na cewa tana sace kayan agaji a Gaza
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon
  • ’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi
  • Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar
  • Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?
  • Madagascar Ta Sanar da Kafa Sabuwar Gwamnati Tare da Manyan ‘Yan Adawa
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari