Kashe mutane 5 da sace Hakimi da limamai ya fusata Sakkwatawa
Published: 1st, September 2025 GMT
’Yan gudun hijira daga sama da kauyukka 10 a Ƙaramar Hukumar Shagari ta Jihar Sakkwato sun rufe hanyar Shagari zuwa Sakkwato domin nuna fushinsu ga gwamnati kan azabar da suke sha hannun ’yan bindiga a yankinsu.
Mata da mazan sun buƙaci daukin gwamnati kan abin da ke addabar su, sun rufe babbar hanyar da ta hada jihohin Sakkwato da Kebbi da Neja.
A yayin zanga-zangar a ranar Lahadi, wani daga ƙauyen Rinaye ya shaida wa Aminiya cewa, “Rashin kulawar da gwamnati ta nuna mana ya sa muka rufe hanyar mota don janyo hankalinta da jami’an tsaro gare mu a ɗauki matakin korar mana ’yan bindigar su bar yankinmu.
“Yau (Lahadi) sun jera kwana uku kullum sai sun zo sun sace mana mutane kuma babu wasu jami’an tsaro da aka kawo mana don kare mu.”
Ya ce ’yan bindigar sun tashi ƙauyuka uku a ranar Juma’a, sun tafi na biyu dana uku a ranar Assabar da Lahadi.
“A garin Rinaye sun sace mai garinmu da duka limaman garin bayan sun kashe mutum uku sun yi garkuwa da wasu mutanen garin da ba a tantance yawansu ba, a wannan Asabar da Lahadi.
“Shekaranjiya sun shiga garin Aske dodo da Tungar Barkenda Jandutse duk waɗannan wurare babu mutane a cikinsu yanzu, sun kashe mutane biyu da yin garkuwa da wasu 15,” a cewar majiyar.
Ya ce hukumomin tsaro da gwamnati ba a abin da suka yi a yanzu, ko jaje ba a kai musu ba.
Malama Tunba mai yara biyar mata uku da maza biyu daga ƙauyen Jandutse ta ce yanzu haka ba ta san inda ’ya’yanta suke ba tun da suka gudu a ranar Assabar, a haka ta yini ba abin da ta sa a bakinta.
Tumba ta yi kira ga gwamnati ta taimaka musu da tsaro mu zauna a gidajensu cikin rufin asiri, wahalar da suke ciki ta yi yawa.
Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) da ta jiha SEMA sun ce sun san da zaman ’yan gudun hijirar da suka gudu kan matsalar ’yan bindiga.
Bayanin ya ce, “A Ƙaramar hukumar Shagari ɗaruruwan mutane sun bar muhallansu kan rashin tsaron da ya kunno kai a yankin suna neman ɗauki.
“Don ganin halin da ake ciki, hukumomin sun tafi rukunin gidaje 30 a ƙaramar hukumar inda mutanen suka zauna sun tuntubi hakiman mutanen daga cikinsu akwai Hakimin ‘Yan Dundaji, Malam Muhammad Bello Magaji, da Maigarin Tungar-Barke, Muhammadu Tudu, wanda ya tabbatar da harin da aka kai musu kwana uku baya, yana da ’yan gudun hijira da yawa.
Sauran ƙauyukan da abin ya shafa sun haɗa da Tungar-Barke, Lungu, Aske-Dodo, Tungar-Doruwa, Zango, ‘Yan Yandu, Tungar Na’anza, Ila, da sauransu.
A halin da ake ciki hukumomin na kira ga gwammati ta kawo ɗaukin gaggawa musamman samar da tsaro a ƙauyukan don mutanen su koma gidajensu cikin aminci.
Wakilinmu ya tuntubi shugaban karamar hukumar Shagari Honarabul Alhaji Maidawa sai dai bai samu jin ta bakinsa ba har zuwa haɗa labarin.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Kungiyar Kare Hakkokin Bil’Adama Ta Siriya Ta Bankado Karin Fararen Hula Da Aka Kashe A Rikicin Suweida
Kungiyar Kare Hakkokin Dan Adam ta Siriya ta bayyana sabbin mutanen da suka mutu sakamakon harin Suweida
Kungiyar kare hakkin dan adam ta Siriya (SOHR) ta bayyana wasu sabbin fararen hula tara da aka ci zarafinsu a lokacin abubuwan da suka faru a Suweida a watan Yulin da ya gabata.
Hukumar da ke sa ido kan lamarin ta bayyana cewa, wadanda aka kashen da suka hada da mata biyu, an kashe su ne a filin wasa a lokacin da wasu ma’aikatun tsaro da na cikin gida na gwamnatin rikon kwarya suke lardin na Suweida, tare da halartar mayakan ‘yan kabilar Larabawan Bedouin.
Hukumar da ke sa ido kan lamarin ta ce adadin mutanen da suka mutu a watan Yulin da ya gabata a tsakanin al’ummar Druze a Suweida ya kai 1,592, yayin da adadin wadanda suka mutu tun safiyar Lahadi 13 ga watan Yuli, sakamakon arangama, da kisa a fili, da kuma harin bama-bamai da sojojin mamayar Isra’ila suka kai ya kai 2,047.
Hukumar da ke sa ido kan lamarin ta yi bayanin cewa, “a ci gaba da bincike, akwai yiyuwar adadin wadanda suka mutu ya karu, ganin cewa akwai wadanda suka bace daga irin wadannan abubuwan da har yanzu ba a tantance makomarsu ba.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Tawagar Yan Wasan Damben Gargajiya Ta Iran Ta Zama Zakara A Damben Ta Duniya September 16, 2025 An Fara Taron Hukumar Makamashin Nukliya Ta Duniya IAEA Karo Na 69 A Birnin Vienna September 16, 2025 Espania Ta Soke Cinikin Makamai Na EUR Miliyon 700 Da HKI Saboda Kissan Kiyashi A Gaza September 16, 2025 Makaman ‘Drons’ Na Yemen Sun Fada Kan Wurare Masu Muhimmanci A HKI September 16, 2025 Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila September 16, 2025 Ministan Tsaron Venezuela Ya Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Juyin Mulki A Kasar September 16, 2025 Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya September 16, 2025 Bayanin Bayan Taron Doha Ya Yi Kira Da A Kafa Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kare Kai September 15, 2025 Fira Ministan Spain: Bai Kamata A Rika Barin “Isr’ila” Tana Shiga Gasar September 15, 2025 Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Sarkin Kasar Qatar A Birnin Doha September 15, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci