ECOWAS na shirin kafa rundunar yaki da ta’addanci mai dakaru 260,000
Published: 26th, August 2025 GMT
Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Yammacin Afirka ta ECOWAS ta bayyana shirinta na kafa rundunar yaki da ta’addanci mai dauke da sojoji 260,000 domin tunkarar barazanar tsaro da ke kara ta’azzara a yankin.
Shugaban ECOWAS, Omar Alieu Touray, wanda wakilinsa Abdel-Fatau Musah ya gabatar da jawabi a taron shugabannin rundunonin tsaro na Afirka da aka gudanar a Abuja, ya ce wannan mataki na daga cikin kokarin dakile ayyukan ta’addanci da sauran matsalolin tsaro da suka addabi yankin.
“Babu wani yanki a Afirka da ya tsira daga ta’addanci, rikice-rikicen cikin gida da kuma koma-baya ta fannin ci-gaba,” in ji Musah.
ECOWAS ta ce za ta bukaci dala biliyan 2.5 a kowace shekara domin tallafa wa rundunar da kayan aiki da kudaden gudanarwa. Ana sa ran Ministocin kudi da na tsaro za su gana a ranar Juma’a domin kammala tsarin yadda za a samar da kudaden.
Touray ya ce yankin Sahel ya fi kowanne yanki fama da ta’addanci, inda ya ce kashi 51 cikin 100 na mutanen da suka mutu sakamakon ta’addanci a duniya a shekarar 2024 sun fito ne daga yankin.
A yayin da ECOWAS ke ci gaba da kokarin kafa rundunar sojoji 5,000 karkashin tsarin tsaro na Afirka, ana sa ran sabuwar rundunar za ta taimaka wajen kara karfin yaki da ta’addanci.
Nijar ta halarta, Mali da Burkina Faso sun kauraceSai dai ba dukkan kasashen da aka gayyata suka halarci taron ba. Daga cikin kasashe 54 da aka gayyata, 36 ne suka samu wakilci.
Ko da yake Jamhuriyar Nijar ta halarta, Mali da Burkina Faso ba su halarta ba — lamarin da ba zai rasa nasaba da rikicin siyasa da ke tsakaninsu da ECOWAS ba.
Tsohon Firaministan Guinea, Lansana Kouyaté, ya bayyana taron a matsayin wani muhimmin mataki na hadin gwiwar tsaro a Afirka.
“Karon farko ne shugabannin rundunonin tsaro na dukkan kasashen Afirka suka hadu. Wannan ya nuna muhimmancin batun — ba za a samu ci gaba ba sai da zaman lafiya,” in ji shi.
Kouyaté ya bukaci shugabannin Afirka da su hada kai wajen samar da tsaro, yana mai jaddada cewa Afirka ba kasa daya ba ce, illa dai hadin gwiwar kasashe masu bambancin tarihi da al’adu. Ya ce zai gabatar da shawarwari kan yadda za a samar da kudaden tsaro ta hanyar hadin gwiwa da masu zaman kansu.
Afirka ke da alhalin kula da tsaronta —MDDA nata bangaren, Mataimakiyar Sakataren Majalisar Dinkin Duniya, Amina Mohammed, ta bukaci shugabannin Afirka da su dauki nauyin tsaron nahiyar.
Ta yi gargadin cewa ta’addanci, yaki ta kafar intanet da sauyin yanayi na barazana ga zaman lafiyar Afirka. Ta kara da cewa, “Afirka ta zama cibiyar mutuwar mutane sakamakon ta’addanci. A cikin shekaru biyu kacal, hare-hare a kasashen gabar tekun yammacin Afirka sun karu da kashi 250 cikin 100.”
Ta ce fiye da makarantu 14,000 sun rufe a yankin Sahel saboda rikici, sannan ta yi gargadi kan barazanar fasahar zamani da sauyin yanayi, ciki har da faduwar ruwan tafkin Chadi da ta raba fiye da mutane miliyan uku da muhallinsu.
Tinubu ya bukaci sabuwar dokar tsaron AfirkaShugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, wanda Mataimakinsa Kashim Shettima ya wakilta, ya bukaci a samar da sabuwar dokar tsaro ta nahiyar Afirka da za ta dogara da amincewa, musayar bayanan sirri da hadin gwiwa.
“Wannan taro bai kamata ya kare da tafi ba kawai watse. Ya zama ginshikin sabuwar tsarin tsaro na Afirka,” in ji shi.
Ya bukaci a kafa taron dindindin na shugabannin rundunonin tsaro na Afirka da kuma zuba jari a fannin kirkire-kirkire na tsaro da fasahar zamani.
A karshe, tsohon shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Farfesa Ibrahim Gambari, ya bayyana cewa akwai fiye da kungiyoyin ’yan tada kayar baya 1,000 a nahiyar Afirka, yana mai kira da a kara karfafa masana’antar tsaro da kirkirar fasahohin gida.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Tsaro yaki da ta addanci tsaro na Afirka
এছাড়াও পড়ুন:
Hamas ta bukaci kasashen musulmi da na Larabawa su dauki mataki mai tsari kan Isra’ila
Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta yi kakkausar suka ga harin da Isra’ila ta kai kan Qatar a baya-bayan nan, inda ta bukaci kasashen Larabawa da na musulmi da su dauki matsaya daya kan matakan wuce gona da iri na gwamnatin mamayar.
Basem Naim, mamba a ofishin siyasa na kungiyar Hamas,ne ya yi wannan kiran a cikin wata sanarwa a ranar Lahadi, yayin da ministocin harkokin wajen kasashen Larabawa da na kasashen musulmi suka halarci taron gaggawa na Doha, domin tattauna harin da Isra’ila ta kai kan shugabannin Hamas a kasar Qatar.
Babban jami’in na Hamas ya yi kira ga shugabannin yankin da ke halartar taron da su mayar da Isra’ila saniyar ware a siyasance da ta fuskar tattalin arziki da kuma gurfanar da jami’an Isra’ila a kotunan duniya domin kawo karshen yakin kisan kare dangi a Gaza.
Naim ya kuma jaddada cewa, harin da Isra’ila ta kai kan tawagar Hamas a birnin Doha, ya zo ne a daidai lokacin da tawagar ke tantance wata sabuwar shawarar tsagaita bude wuta a Gaza.
“Mun nuna sassauci mafi girma na kawo karshen kisan kiyashin da ake yi a Gaza, amma sojojin mamaya ne, ta hanyar amfani da kisa da kuma sanya sharuddan nasu, ke kawo cikas ga duk wata yarjejeniya da za a iya cimma.”
Daga karshe ya bayyana cewa kungiyar Hamas tana sa ran taron zai dauki matsaya guda daya mai ma’ana tsakanin Larabawa da musulmi, da suka hada da tsagaita bude wuta nan take da kawo karshen yakin Gaza, da dage shingen da aka yi, da yanke duk wata alaka da Isra’ila, da gurfanar da isra’ila kan laifuffukan da ta aikata, da samar da falasdinu mai ‘yancin cin gashin kai, da Al-Quds a matsayin babban birninta, da kuma tabbatar da ‘yancin komawar ‘yan gudun hijira.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Rabin Sojojin Isra’ila da suka ji rauni a yakin Gaza na fama da ciwon damuwa September 15, 2025 Sudan ta soki takunkuman da Amurka ta kakaba mata September 15, 2025 Dakarun Sojin Yamen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Ramon Na Isra’ila. September 14, 2025 Isra’ila Za ta Gamu Da Mummunar Martani Idan Tayi Gigin Afkawa Iran September 14, 2025 Ministocin Harkokin Wajen Kasashen Larabawa Da Na Musulmi Sun Fara Taro A Qatar. September 14, 2025 Gwamnatin Najeriya Ta Sanar Da Sabon Sharadi Na Bude Asusun Banki September 14, 2025 An Zabi Issa Tchiroma A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A Kamaru September 14, 2025 Kasar Iran Ta Yi Fatali Da Zarge-Zargen Da Kungiyar G7 Da Kawayenta Suka Yi Kanta September 14, 2025 Iran Ta Bayyana Shirinta Na Halartar Taron Shekara-Shekara Na Hukumar Makamashin Nukiliya September 14, 2025 Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Bayyana Rashin Halarta Tawagarta A Kada Kuri’a Kan Batun Falasdinu September 14, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci