Aminiya:
2025-11-02@19:08:13 GMT

Yau ake cika shekaru 10 da ƙirƙirar Ranar Hausa

Published: 26th, August 2025 GMT

A duk ranar 26 ga watan Agustan kowace shekara ake bukukuwan zagayowar Ranar Hausa ta Duniya.

An fara wannan biki ne tun a shekarar 2015, inda wani tsohon ma’aikacin sashen Hausa na BBC kuma ma’aikacin TRT Hausa a yanzu, Abdulbaƙi Jari Aliyu ya ƙirƙiro tare da wasu masu amfani da shafukan sada zumunta.

An ɓullo da ranar ce domin haɗa kan masu magana da harshen Hausa a faɗin duniya da nufin magance matsalolin da ke ci musu tuwo a ƙwarya.

Da farko dai, an fara bikin wannan rana ce kamar wasa a shafukan sada zumunta, inda aka yi ta amfani da kalmar #RanarHausa. Zuwa shekara ta 2018 kuma aka fara yin bikin a zahiri tare da gudanar da tarurruka da shagulgula a garuruwa a faɗin Najeriya da ma wasu ƙasashen irinsu Ghana.

NAJERIYA A YAU: Ci Gaban Da Harshe Da Al’adun Hausa Suka Samu A Shekaru 10 PDP ta miƙa wa kudancin Najeriya takarar shugaban ƙasa a 2027

Masu shirya bikin ranar suna ƙoƙarin ganin sun bayyana mahimmancin harshen Hausa da yadda za a ci gaba da yaɗa shi. Haka kuma a kan tattaro masana da masu bincike domin yin nazari kan wasu sabbin abubuwa da ya kamata a sani da Hausa.

A shekaru biyu da suka shuɗe, an yi bikin Ranar Hausa ta Duniya a ƙasashe sama da 20, ciki har da Faransa da Saudiyya.

Masu fafutukar wannan rana suna fatan cewa nan gaba za a amince da yaren Hausa a hukumance a ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU) da kuma ƙungiyar raya ƙasashen yammacin Afrika (ECOWAS).

Wane ci-gaba aka samu?

A wannan shekarar dai za a yi gagarumin bikin wannan rana a garin Daura da ke Jihar Katsina, wajen da ake kallo a matsayin tushen Hausa da al’ummar Hausawa. 

Za a yi tattaunawa da kuma nuna al’adu tare da mahalarta daga ƙasashe daban-daban a yammacin Afirka da kewaye.

Abdulbaƙi Aliyu Jari, wanda shi ne jagoran wannan taro na Ranar Hausa ta Duniya, ya shaida wa Aminiya cewa, a yanzu haka bincike ya ayyana harshen Hausa a matsayin yare na 11 da ake aka fi amfani da shi a faɗin duniya, kuma ana sa ran nan da shekarar 2050 zai zama na biyar a duniya. 

“Hausa ba kamar sauran yaruka ba ne da suke ɓacewa, Hausa na ƙara bunƙasa. Ana magana da yaren a nahiyar Afirka tsakanin mutane fiye da miliyan 170,” in ji shi.

Ya bayyana cewa, Hausa ya riga da ya samu gurbi na musamman a Jamhuriyar Nijar, inda kaso sama da 80 na al’ummarsu ƙasar suke magana da yaren, haka ma a ƙasar Ghana. Kafofin yaɗa labarai ma tuni suka rungumi harshen Hausa domin isar da saƙonninsu ga ɗimbin mabiya a faɗin duniya.

Jari ya ce, sun faro wannan lamari ne kamar wasa a shekarar 2015, amma sai ga shi yanzu duk duniya ana maganar sa. “Abu ne da aka faro a shafukan sada zumunta, sai ga shi yanzu ana bikin a ƙasashe kusan 25”.

A cewar Jari, Ranar Hausa ta Duniya, “Ba wai biki ba ce kawai, a’a, wata hanya ce da masu magana da harshen Hausa a duk faɗin Najeriya, Afirka ta Yamma da sauran ƙasashen duniya za su haɗa kai, su tattauna ƙalubalen da ke damun su da kuma samar da zaman lafiya.”

Da yake tsokaci kan nasarorin da aka samu a cikin shekaru goma da suka gabata, ya bayyana cewa a halin yanzu bikin ranar Hausa ya samu wani gurbi  a kalandar masu magana da harshen Hausa a duk duniya.

Jari ya yi kira ga gwamnatocin Afirka, musamman a Najeriya da Afirka ta Yamma, da su amince da Hausa a matsayin harshen ƙasa ko na yanki a hukumance, ta hanyar yin koyi da Jamhuriyar Nijar inda ake magana da Hausa a hukumance.

Hakan a cewarsa zai yara al’adu taro da tabbatar da wanzuwar zaman lafiya.

Su wane ne Hausawa?

Ana kallon al’ummar Hausawa a matsayin ɗaya daga cikin ƙabilu masu muhimmanci a yammacin Afirka, da al’adunsu na musamman a faɗin nahiyar da ma sauran ƙasashen duniya. Yayin da wasu alƙaluma suka ce adadin Hausawa ya kai kimanin miliyan 150, Farfesa Muhammad Bunza na Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo da ke Sakkwato na ganin cewa adadin zai iya haura miliyan 500 idan aka haɗa da masu magana da yare biyu.

Ba a iya Najeriya ake samun al’ummar Hausawa ba, baya ga Nijar akwai ƙasashe irin su Saudiyya, Sudan, Maroko, Libya, da Mali, inda suke zuwa kasuwanci, ko kuma a kan haɗu ta dalilin auratayya.

A wata hira da BBC Hausa a shekarar 2023, Farfesa Bunza ya  bayyana cewa tsawon shekaru aru-aru, auratayya tsakanin ƙabilu da Hausawa ta sa su rikiɗewa zuwa ƙabila guda.

A yanzu dai, harshen Hausa yana cikin jerin harsunan da ake magana da su a duniya, inda wasu suka ce na bakwai a duniya, kuma yana ci gaba da samun karɓuwa. Amma duk da haka, Farfesa Bunza ya yi gargaɗin cewa harshen yana fuskantar ƙalubale, ciki har da ƙarancin koyar da shi a makarantu da rashin malamansa.

Ya buƙaci gwamnatocin Afirka da su haɓaka amfani da harshen, yana mai cewa, “Baya ga Swahili, babu wani yare na Afirka da zai iya yin gogayya da Hausa.

Yadda yaren Hausa ya bunƙasa

Masana harshe da dama na yi wa harshen Hausa kallon wani harshe mai yaɗuwa a faɗin duniya, inda yanzu haka nazarce-nazarce ke nuna cewa Hausa ne harshe na 11 a fadin duniya wajen yawan masu amfani da shi, kuma na ɗaya a Afirka ta yamma.

Sai dai akwai jayayya tsakanin manazarta kan girman Hausa a nahiyar Afirka, inda wasu ke ganin harshen Swahili da ake yi a ƙasashe da dama na yankin Afirka maso Gabas ya ɗara na Hausa wanda ake yi a yankin Afirka ta yamma da Afirka ta Tsakiya da ma kusurwar Afirka.

Sai dai nazarce-nazarce sun nuna harshen Hausa yana gaba da na Swahili ta fannin yawan masu yin amfani da shi inda shi kuma Swahili ke gaba wajen yawan ƙasashen da ake yin yaren.

Tuni dai manyan kafafe irin su Facebook da Google suke amfani da harshen Hausa inda tuni manhajar amfani ta Android da IOS suka shigar da shi cikin harsunan da suke amfani da su.

Ko a baya-bayan nan sai da hukumar Lafiya ta Duniya ta sanya Hausa a cikin harsuna guda uku da ta zaɓa domin yaki da annobar korona a Afirka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hausawa Najeriya Ranar Hausa ta Duniya Ranar Hausa ta Duniya da harshen Hausa a faɗin duniya harshen Hausa a ranar Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Wadi Al-Salam: Maƙabartar Musulmai Mafi Girma A Duniya

Imam Ali shi ne halifan Annabi Muhammad na hudu a mahangar Ahlussunnan, amma mabiya mazhabar Shi’a na daukar sa a matsayin na farko daga cikin imamansu 12.

Wannan ya sanya akasarin mabiya Shi’a na Iraki kan bukaci a binne su a makabartar, kuma sanadiyyar saukin sufuri a zamunnan baya-bayan nan, wasu mabiya Shi’a daga kasashen duniya kan so a binne su a makabartar.

Tsarin makabartar ya kasance cakuduwa ce ta gine-ginen hubbarai irin na zamanin baya, da hanyoyi masu tsuku da suka ratsa ta cikinta da kuma wasu wurare da ake yi wa kallon masu tsarki.

 

Me ya sa ake kiran makabartar Wadi al-Salam?

Ana kiran makabartar da sunan Wadi al-Salam, wato ‘kwarin aminci’ ne saboda dalilai na tarihi da dama.

Dalilai na addini: Ana yi wa makabartar daukar mai daraja, tare da imanin cewa wadanda ke kwance a cikinta na cikin rahama.

Alaka da Imam Ali: Makabartar tana makwaftaka da kabarin Imam Ali bin Abi Talib a birnin Najaf, wanda hakan ya sa Musulmai, musamman mabiya akidar Shi’a ke girmama ta kuma suke kwadayin ganin an binne su a cikinta.

Girma: Makabartar ta kasance mafi girma a duniya, inda ta mamaye wuri mai girman gaske, kunshe da miliyoyin kaburbura, inda ta zamo tamakar wani birni na mamata.

Ziyara: Masu ziyara zuwa birnin Najaf, mai tsarki ga mabiya akidar Shi’a sukan bi ta cikin makabartar tare da karanta Fatiha da kuma yin addu’o’in samun rahama ga wadanda ke kwance, lamarin da ya mayar da wurin tamkar wuri na ziyarar ibada.

Wadannan dalilai ne suka sanya tuntuni aka yi wa wurin lakabi da ‘kwarin aminci’ tun asali, kuma ake ci gaba da kiranta da hakan har yanzu.

 

Tarihin kafuwar makabartar Wadi al-Salam

Makabartar ta samo asali ne tun kafin zuwan addinin Musulunci a lokacin Annabi Muhammad, inda tun kafin wancan lokaci ake binne mutane a wurin.

Wuri ne mai muhimmanci wanda ke karbar bakuncin masu bincike na kimiyya da masana addini, musamman mabiya Shi’a daga sassa daban-daban na duniya.

Wadi al-Salam na da kofofi da dama da ake bi wajen shigar ta, inda hakan ke saukake zirga-zirga ga masu ziyara, kuma yawancin wadannan kofofi na karuwa ne bisa fadadar makabartar.

A shekara ta 2016 ne Hukumar kula da ilimi da al’adu ta Majalisar Dinkin Duniya ta ayyana makabartar a matsayin daya daga cikin wuraren tarihi na duniya.

 

Kalubalen da makabartar ke fuskanta

Daya daga cikin manyan kalubalen da makabartar ke fuskanta shi ne karuwar mutane da ake binnewa a lokacin yaki.

Misali, a lokacin da aka yi fama da rikicin kungiyar ISIS a Iraki, yawan mutanen da ake binnewa a kowace rana a makabartar ya daga zuwa 150 ko 200 a kowace rana, daga gawa 80 zuwa 120 da aka saba.

Wannan ya sanya wuraren binne sabbin mamata ya yi karanci.

 

Farashin binne mamaci

Farashin binne mamaci a makabartar Wadi al-Salam ya danganta ne da lokaci da kuma halin da ake ciki na zaman lafiya.

Ya zuwa farkon shekara ta 2025, kudin sayen filin binne mamaci mai girman murabba’in mita 25 ya kai miliyan biyar na kudn kasar Iraki, wato kimanin Dala 4,100, inda hakan ya nunka farashin da ake biya a lokutan da ake zaman lumana sosai.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka November 2, 2025 Manyan Labarai An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano November 2, 2025 Manyan Labarai Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima November 1, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wadi Al-Salam: Maƙabartar Musulmai Mafi Girma A Duniya
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka
  • Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar
  • Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Tsare-tsaren Ci Gaban Kaduna a Taron Duniya a Dubai.
  • Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?
  • Iran Ta Sanya  Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi
  • Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda