Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka
Published: 26th, August 2025 GMT
Na yi imani babu rayuwa ba tare da harshe ba, domin duk wata al’umma tana da buƙatar harshe domin gudanar da rubuce-rubuce, kimiyya da fasaha.
Amma an yi sakaci da nazarin harshen Hausa, duk da cewa yana cikin manyan harsunan duniya masu ƙarfi da adabi.
Don haka zan fara bayyana matsalolin, sannan in kawo shawarwari.
Idan gwamnati da manyan al’umma ba su ɗauki Hausa da muhimmanci ba, ba zai samu ci gaba ba. An taɓa samun shugaban ƙasa da ya ce nazarin wasu darusa ɓata lokaci ne, amma shi kansa a lokacin yaƙin neman zaɓe da Hausa yake magana.
Gwamnati ta nuna rashin kulawa da harshen Hausa, tana ganin ba shi da amfani. Alal misali:
1. Mayar da Hausa “zaɓi” a sakandire.
2. Tsaurara sharuɗa wajen shiga jami’a domin nazartarsa.
3. Rashin bayar da tallafin karatu kamar yadda ake yi wa wasu harsuna.
Matsala ta biyu: Ka Ƙi Naka, Duniya Ta So ShiDa yawa daga cikin Hausawa ba sa alfahari da harshensu. Maimakon su zurfafa a kansa, sai ƙasashen waje suka ɗauki Hausa suna koyarwa a jami’o’in duniya. Haka kuma, yawancin Hausawa idan suna amfani da shafukan sada zumunta, rubuce-rubucensu da Hausa suke yi, ko littattafan addini sai an fassara musu da Hausa.
Abin kunya ne a ce ƙasar Nijar ta ayyana Hausa a matsayin harshen ƙasa, amma Nijeriya ba ta yi haka ba, duk kuwa da cewa Hausa na daga cikin manyan harsunan ƙasar.
Haka kuma wasu malamai suna sa wa ɗalibai wahala wajen nazarin Hausa, suna ƙauron da su daga koyonsa.
Matsala ta uku: Idan An Bi Ta Ɓarawo…Ya kamata malamai da ɗalibai su ci gaba da aikin fassara kalmomi daga fannoni daban-daban na ilimi zuwa Hausa, don a samu damar shiga kowanne fanni kamar yadda ake yi da Turanci, Larabci, Sinanci da sauransu.
Gudunmuwar Harshen Hausa:1. An fassara kusan duk littattafan addini zuwa Hausa.
2. An fassara littattafan kimiyya, tarihi, lissafi da sauransu.
3. Hausa ta mamaye kafafen sada zumunta kamar Facebook, WhatsApp, X, Instagram da TikTok.
4. Ana amfani da Hausa a kafafen yaɗa labarai a ƙasashe irin su Amurka, Sin da Faransa.
5. Malamai sun rubuta littattafai da muƙaloli da dama domin ci gaban harshen.
Shawarwari:1. A tafiya da zamani wajen koyar da Hausa.
2. A sauƙaƙa hanyoyin koyo da koyarwa.
3. A mayar da Hausa darasi na dole a firamare da sakandire.
4. A wajabta wa ɗaliban ƙasashen waje koyon Hausa idan suka zo karatu a Nijeriya.
5. A shigar da Hausa cikim fannin kimiyya da fasaha.
6. A sa Hausa cikin darussan GES/GSE a jami’o’i da kwalejojin ilimi.
7. A ayyana Hausa a matsayin harshen hukuma a Arewa ko Nijeriya baki ɗaya.
8. A ƙarfafa gwiwar iyaye, abokai da malamai ga ɗaliban da ke nazartar Hausa.
9. A riƙa bai wa masanan Hausa aikin da ya dace da su, musamman fassara da rubuce-rubuce.
Idan aka aiwatar da waɗannan, za a dawo da martabar harshen Hausa.
KammalawaTakardar ta nuna matsalolin da harshen Hausa ke fuskanta, gudunmuwar da yake bayarwa ga al’umma da addini, sannan ta kawo hanyoyin da za a bi don dawo da martabarsa a ƙasar nan.
Mubarak Idris Jikamshi ne ya rubuta albarkacin Ranar Hausa ta Duniya
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Harshe Nazari Gundumawa Ranar Hausa ta Duniya Shawarwari takarda harshen Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Sanya Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3
Gwamnatin kasar Iran ta sanar da ranar 30 ga watan nuwambar kowacce shekara a matsayin ranar kasa ta tsibirin Abu Musa tumbu babba da tumbu karami da ta karbo daga hannu birtaniya a shekaru da suka gabata, wanda yayi daidai da 9 ga watan Azar na kalandar iraniyawa .
Tsibiran guda 3 da ake takaddama akansu Abu musa da tunbu babba da karami suna yankin tekun fasha ne tsakanin mailand na iran da kuma hadaddiyar daular larabawa, tsibbiran wani bangare ne na kasar iran tun karnoni da suka gabata da ke cike da abubuwa da suka safi doka da tarihi a iran da kuma kasa da kasa.
Iran ta jaddada cewa dukkan wadannan tsibirai guda 3 wani bangare na kasarta da babu tantama akai,don haka ta yi kira ga kasashen larabawa da su guji daukar duk wani mataki akai da zai iya cutar da dangantakar dake tsakaninsu.
A ranar 30 ga watan nuwambar shekara ta 1971 ne dakarun birtaniya suka janye daga tsibiran kuma kwana biyu kafin kafa hadaddiyar daular larabawa a hukumance aka dawo da ikon mallakar tsibiran ga kasar iran bisa doka.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka HKI Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza Inda Take Kashe Falasdinawa October 31, 2025 An Tube Yarima Mai Jiran Gado Na Birtaniya Bayan Da Aka Tabbatar Da Laifinsa October 31, 2025 Kasashen Pakistan Da Afghanistan Sun Tsawaita Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta October 31, 2025 M D Duniya Tayi Gargadi Game Da Gwajin Nukiliya Da Amurka Ta Sanar Za ta yi October 31, 2025 Sudan Ta Yi Kira Ga Kwamitin Tsaro Da Ya Ayyana RSF A Matsayin Kungiyar ‘Yan Ta’adda October 31, 2025 Araqchi: Gwajin Makaman Nukiliya Na Amurka Babbar Barazana Ce Ga Duniya October 31, 2025 Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan October 31, 2025 Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Kutsen Na Isra’ila A Kudancin Kasar October 31, 2025 Madagascar Ta Sanar da Kafa Sabuwar Gwamnati Tare da Manyan ‘Yan Adawa October 31, 2025 Iran ta yi fatali da kalamman IAEA Kan Shirin Nukiliyarta October 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci