Sojoji sun kashe manyan Kwamandojin ISWAP 3 a Borno
Published: 6th, June 2025 GMT
Rundunar Operation Hadin Kai (OPHK) da ke samun goyon bayan sojojin sama Air Component sun kashe wasu manyan kwamandojin Kungiyar ISWAP guda uku.
Rundunar ta kashe kwamandojin ne a harin ta’addanci da ba a yi nasara ba a kan Mallam Fatori da ke karamar hukumar Abadam a Jihar Borno.
Sallah: Gwamna Inuwa ya yi kiran sadaukarwa da haɗin kai Gwamnan Akwa Ibom ya sauya sheƙa daga PDP zuwa APCWata majiya mai tushe daga jami’an rundunar ta OPHK ta tabbatar a ranar Alhamis din nan cewa, kwamandojin da aka bayyana sunayensu: Amir Abu Ali Weldone da Amir Ibunu da Amir Abu Waldume, na daga cikin wadanda aka kashe a harin da aka kwashe sa’o’i hudu ana yi a sansanin ‘yan gudun hijira da ke Mallam Fatori.
A cewar majiyoyin, kwamandojin da aka kashe sun taka rawar gani wajen gudanar da ayyukan Kungiyar ISWAP, inda ake kyautata zaton Abu Ali Wadume ne ke jagorantar ayyukan ta’addanci a yankin Kerenoa kusa da kan iyakar Najeriya da Nijar.
Majiyoyin sun tabbatar da cewa, ‘yan ta’addan sun kaddamar da harin hadin gwiwa ne daga yankin Kaniram da sanyin safiyar Laraba, inda suka afkawa sojoji.
Mayakan ISWAP sun yi amfani da manyan makaman yaki hade da jirage marasa matuki ciki har da makamin (AGLs), amma sun gamu da turjiya daga sojojin kasa na rundunar ta OPHK da goyan bayan manyan makaman yaki da suka hada da tankokin yaki da suka rika amfani da su babu kakkautawa.
Majiyar na cewar sojojin sun samu nasarar dakile harin bayan kazamin fadan da ya tilastawa maharan ja da baya cikin rudani a gaggauce.
Rahoton na cewar, akalla ‘yan tada kayar baya 12 ne aka tabbatar da mutuwarsu, tare da kwato bindigogin AK-47 guda bakwai, manyan bindigogi guda uku samfurin (GPMGs), da makaman roka guda biyu (RPGs), da wasu bama-bamai.
“Har yanzu ana ci gaba kididdige barnar da aka yi wa ‘yan ta’addan, amma an tabbatar da kashe wadannan manyan kwamandojin guda uku da aka ambata sunayensu wanda kuwa hakan babbar nasara ce tga kokarin da mayakan sojojin Najeriya ke samu akan ‘yan ta’addan.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: kungiyar ISWAP
এছাড়াও পড়ুন:
Masu Garkuwa Da Mutane Sun Dira Jihar Kogi, Sun Sace Wani Basarake
Ƴansandan jihar Kogi sun tabbatar da sace wani basarake mai suna Samuel Ajayi Bello yayin da yake aikin gona a gidan gonarsa na Ponyan da ke kan titin Ponyan-Irele, a ƙaramar hukumar Yagba ta Gabas.
Mai magana da yawun ‘yansandan jihar, SP William Aya, ya bayyana cewa lamarin ya faru ne da ƙarfe 10 na safe a ranar Litinin. Ya kuma ce Kwamishinan ‘yansandan jihar ya tura rundunar ta musamman don taimakawa wajen gudanar da bincike da kuma ceto wanda aka sace.
Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Afirka Sun Yi Alkawarin Karfafa Alaka Ƴan Bindiga Sun Kai Farmaki Kwara, Sun Kashe Mutum 1, Sun Ƙona GidajeShugaban ƙungiyar ci gaban yankin Ponyan, Hon. Banjo Fabola, ya tabbatar da cewa an sace Ajayi ne tsakanin karfe 9 zuwa 10 na safe, inda ‘yansanda da ‘yan sa kai suka fara bincike a dazuzzukan yankin.
Akwai bayanin cewa wasu sassan jihar na fama da hare-haren ‘yan fashi a baya-bayan nan, inda wasu mutane suka mutu yayin da ake sace-sace. Duk da haka, Kwamishinan yaɗa labarai na jihar, Kingsley Fanwo, ya tabbatar da cewa gwamnati na ɗaukar matakai don magance wannan matsala.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp