Aminiya:
2025-09-18@01:16:27 GMT

Sojoji sun kashe manyan Kwamandojin ISWAP 3 a Borno

Published: 6th, June 2025 GMT

Rundunar Operation Hadin Kai (OPHK) da ke samun goyon bayan sojojin sama Air Component sun kashe wasu manyan kwamandojin Kungiyar ISWAP guda uku.

Rundunar ta kashe kwamandojin ne a harin ta’addanci da ba a yi nasara ba a kan Mallam Fatori da ke karamar hukumar Abadam a Jihar Borno.

Sallah: Gwamna Inuwa ya yi kiran sadaukarwa da haɗin kai Gwamnan Akwa Ibom ya sauya sheƙa daga PDP zuwa APC

Wata majiya mai tushe daga jami’an rundunar ta OPHK ta tabbatar a ranar Alhamis din nan cewa, kwamandojin da aka bayyana sunayensu: Amir Abu Ali Weldone da Amir Ibunu da Amir Abu Waldume, na daga cikin wadanda aka kashe a harin da aka kwashe sa’o’i hudu ana yi a sansanin ‘yan gudun hijira da ke Mallam Fatori.

A cewar majiyoyin, kwamandojin da aka kashe sun taka rawar gani wajen gudanar da ayyukan Kungiyar ISWAP, inda ake kyautata zaton Abu Ali Wadume ne ke jagorantar ayyukan ta’addanci a yankin Kerenoa kusa da kan iyakar Najeriya da Nijar.

Majiyoyin sun tabbatar da cewa, ‘yan ta’addan sun kaddamar da harin hadin gwiwa ne daga yankin Kaniram da sanyin safiyar Laraba, inda suka afkawa sojoji.

Mayakan ISWAP sun yi amfani da manyan makaman yaki hade da jirage marasa matuki ciki har da makamin (AGLs), amma sun gamu da turjiya daga sojojin kasa na rundunar ta OPHK da goyan bayan manyan makaman yaki da suka hada da tankokin yaki da suka rika amfani da su babu kakkautawa.

Majiyar na cewar sojojin sun samu nasarar dakile harin bayan kazamin fadan da ya tilastawa maharan ja da baya cikin rudani a gaggauce.

Rahoton na cewar, akalla ‘yan tada kayar baya 12 ne aka tabbatar da mutuwarsu, tare da kwato bindigogin AK-47 guda bakwai, manyan bindigogi guda uku samfurin (GPMGs), da makaman roka guda biyu (RPGs), da wasu bama-bamai.

“Har yanzu ana ci gaba kididdige barnar da aka yi wa ‘yan ta’addan, amma an tabbatar da kashe wadannan manyan kwamandojin guda uku da aka ambata sunayensu wanda kuwa hakan babbar nasara ce tga kokarin da mayakan sojojin Najeriya ke samu akan ‘yan ta’addan.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: kungiyar ISWAP

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano

Hukumar Kula da Inshorar Lafiya ta Kasa (NHIA) a ranar Laraba ta kaddamar da shirin bayar da kulawar lafiyar gaggawa kyauta ga yara a Asibitin Koyarwa na Aminu Kano (AKTH), Kano.

Shirin, a cewar Darakta a hukumar, Dr. Salahudeen Sikiru, wani bangare ne na fadada shirin lafiyar iyaye da NHIA ke aiwatarwa zuwa ga yara masu rauni da masu bukata ta musamman.

Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo Ana zargin mace da kashe ’yar uwarta a kan N800 din barkono

Ya ce an fara shirin fiye da shekara ɗaya da ta gabata da nufin rage mace-macen jarirai ’yan kasa da shekaru biyar.

“Mun fara wannan shiri fiye da shekara guda da ta gabata da nufin rage mace-macen jarirai. Yanzu mun zo nan don fara na ɓangaren jarirai. Mu za mu biya kudin kulawar gaggawar yaran sannan mu tabbatar an kula da su har su samu ingantacciyar lafiya,” in ji Dr. Sikiru.

Ya kuma ce a karkashin shirin, yara da ke fama da matsalolin gaggawa kamar rashin numfashi, amosanin jini, cutar shawara da yaran da aka haifa bakwaini da ma cututtukan da ke buƙatar tiyata za su samu kulawa kyauta.

Ya ce asibitoci za su fara ba da kulawa da zarar an kawo yara, sannan su tura adadin kuɗin kula da yaran a kowanne mako ga NHIA don a biya su.

Daraktan ya kara da cewa duk yaran da ya sami kulawar gaggawar kuma, za a saka shi cikin shirin inshorar lafiya na NHIS, inda hukumar za ta ci gaba da biyan kudin inshorar don tabbatar da samun kulawar lafiya mai inganci.

“Kafin yaro ya ci gajiyar shirin, dole ne a tantance shi a a tabbatar yana da rauni da kuma ba zai iya biyan kuɗin asibiti ba. Haka nan dole ne yaro ya mallaki Lambar Shaida ta Kasa (NIN) don tabbatar da gaskiya da shigar da su cikin tsarin,” in ji shi.

Dr. Sikiru ya kuma ce, “Shiri ne kula da marasa lafiya cikin gaggawan. Da zarar sun zo, za a duba su. Asibitin sai ya turo mana jimillar adadin kudin, mu kuma mu biya.”

Ya ce wannan shiri wani bangare ne na kudurin gwamnatin tarayya na rage mace-macen jarirai da tabbatar da cewa babu yaron da ya rasa kulawar asibiti saboda rashin kudi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 
  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa
  • Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano
  • Ana zargin mace da kashe ’yar uwarta a kan N800 din barkono
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Iran Ta Gabatar Da Sabbin Kayayyaki Guda 5 A Wajen Taron Kolin kere-kere .
  • Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo
  • ’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote
  • Rabin Sojojin Isra’ila da suka ji rauni a yakin Gaza na fama da ciwon damuwa