Aminiya:
2025-06-19@19:16:06 GMT

Kwamishina ya yi murabus saboda sauya sheƙar Gwamnan Akwa Ibom

Published: 6th, June 2025 GMT

Kwamishinan Harkoki na Musamman a Jihar Akwa Ibom, Mista Ini Ememobong, ya yi murabus daga muƙaminsa biyo bayan sauya sheƙar Gwamna Umo Eno daga jam’iyyar PDP zuwa APC.

Wannan na zuwa ne bayan gwamnan ya fice daga jam’iyyar PDP zuwa jam’iyyar APC.

Sallah: Gwamna Inuwa ya yi kiran sadaukarwa da haɗin kai Tinubu ba zai canza Kashim a matsayin mataimakinsa ba a 2027 – APC

Gwamna Eno ya faɗa wa kwamishinoninsa cewa duk wanda ba ya son bin sa zuwa APC ya ajiye aikinsa.

Ememobong, ya ce yana girmama ra’ayin gwamnan, amma ba zai iya binsa APC ba.

“Ba zan iya yin wannan tafiya ba,” in ji Ememobong.

“Na yarda da siyasar aƙida. Na gode wa gwamna bisa ƙauna da ya nuna min, amma dole na tsaya kan abin da nake da yaƙini a kai.”

A ranar Juma’a ne, Gwamna Eno, ya sanar da ficewarsa daga PDP zuwa APC, inda ya ce ya yanke hukuncin ne bayan dogon nazari.

“Na tuntuɓi mutane daga ko ina a cikin jihar,” in ji Eno.

“Wannan shawara ce da ta dace da lokacin da muke ciki. Mun shiga APC ba don mu samu rauni ba, sai don mu ƙara ƙarfi.”

Da wannan sauyin, APC na da iko a jihohi huɗu cikin shida da ke yankin Kudu Maso Gabas, sai Jihohin Ribas da Bayelsa kawai suka rage a hannun PDP.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Akwa Ibom Kwamishina Sauya Sheƙa Siyasa

এছাড়াও পড়ুন:

Litar fetur za ta iya komawa N1,000 a Najeriya saboda yakin Isra’ila-Iran – Masana

Masana sun yi gargadin cewa yakin da ake gwabzawa a tsakanin Isra’ila da Iran zai iya shafar farashin man fetur a duniya kuma hakan zai iya yin illa ga tattalin arzikin Najeriya.

Masanan na cibiyar Commercio Partners da ke Legas sun  bayyana fargabar ce a cikin wani rahoto da cibiyar ta fitar mai taken: “Farashin kayayyaki ya sauka a Najeriya a watan Mayu, amma akwai matsala a nan gaba” wanda aka wallafa shi ranar 16 ga watan Yunin 2025.

A cewar rahoton, rikicin da ake fama da shi a yankin Gabas ta Tsakiya zai iya rage yawan man fetur din da ake samarwa a duniya wanda kuma zai kai ga tashin farashinsa a kasuwanni.

Ma’aikatan Kwalejin Ilimi ta jihar Kaduna za su tsunduma yajin aiki Ambaliyar Mokwa – Har yanzu muna neman mutum 700 – Gwamnatin Neja

Sun yi gargadin cewa duk da yake Najeriya kasa ce mai arzikin man na fetur, amma tashin farashin ba lallai ne ya zama alheri ga kasar ba.

Aminiya ta rawaito cewa farashin danyen mai ya rika yin tashin gwauron zabo a ’yan kwanakin nan inda ya haura Dalar Amurka 75 kan kowacce ganga.

Sai dai tashin na nufin farashinsa zai tashi a gida Najeriya, inda farashin zai iya kaiwa Naira 1,000.

A yanzu dai ana sayar da man ne daga tsakanin N870 zuwa N920 a gidajen mai.

“A Najeriya kuwa, inda yanzu aka janye tallafin man fetur kuma farashinsa ya ta’allaka da kasuwar duniya, hakan zai iya shafar tattalin arzikin kasar,” in ji masanan.

Rahoton ya kuma ce duk da cewa matatar mai ta Damngote na aiki, duk da haka kasar ba ta tsira daga barazanar ba.

Ya kuma ce, “Har yanzu shigo da mai ake zuwa Najeriya, kuma tashin farashinsa a kasuwannin duniya na nufin yadda ake tace shi da rarrabawa ko dakon shi su ma za su karu

“Idan danyen man ya kara tsada, farashin man fetur a Najeriya – wanda yanzu haka yake wajen N825 – zai iya komawa kusan N1,000,” kamar yadda masanan suka yi hasashe.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
  • Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo Ya Karyata Sauya Sheƙa Zuwa APC
  • Ba Atiku kaɗai ba ne matsalar PDP — Gwamna Lawal
  • Nasarorin Gwamna Lawal A Zamfara Abin Mamaki Da Alfahari Ne – Obasanjo
  • Litar fetur za ta iya komawa N1,000 a Najeriya saboda yakin Isra’ila-Iran – Masana
  • Ambaliyar Mokwa – Har yanzu muna neman mutum 700 – Gwamnatin Neja
  • Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 
  • DAGA LARABA: Ko Kare Kai Daga Harin ‘Yan Ta’adda Zai Kawo Karshen Matsalar Tsaro?
  • Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada
  • Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga