Kwamishina ya yi murabus saboda sauya sheƙar Gwamnan Akwa Ibom
Published: 6th, June 2025 GMT
Kwamishinan Harkoki na Musamman a Jihar Akwa Ibom, Mista Ini Ememobong, ya yi murabus daga muƙaminsa biyo bayan sauya sheƙar Gwamna Umo Eno daga jam’iyyar PDP zuwa APC.
Wannan na zuwa ne bayan gwamnan ya fice daga jam’iyyar PDP zuwa jam’iyyar APC.
Sallah: Gwamna Inuwa ya yi kiran sadaukarwa da haɗin kai Tinubu ba zai canza Kashim a matsayin mataimakinsa ba a 2027 – APCGwamna Eno ya faɗa wa kwamishinoninsa cewa duk wanda ba ya son bin sa zuwa APC ya ajiye aikinsa.
Ememobong, ya ce yana girmama ra’ayin gwamnan, amma ba zai iya binsa APC ba.
“Ba zan iya yin wannan tafiya ba,” in ji Ememobong.
“Na yarda da siyasar aƙida. Na gode wa gwamna bisa ƙauna da ya nuna min, amma dole na tsaya kan abin da nake da yaƙini a kai.”
A ranar Juma’a ne, Gwamna Eno, ya sanar da ficewarsa daga PDP zuwa APC, inda ya ce ya yanke hukuncin ne bayan dogon nazari.
“Na tuntuɓi mutane daga ko ina a cikin jihar,” in ji Eno.
“Wannan shawara ce da ta dace da lokacin da muke ciki. Mun shiga APC ba don mu samu rauni ba, sai don mu ƙara ƙarfi.”
Da wannan sauyin, APC na da iko a jihohi huɗu cikin shida da ke yankin Kudu Maso Gabas, sai Jihohin Ribas da Bayelsa kawai suka rage a hannun PDP.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Akwa Ibom Kwamishina Sauya Sheƙa Siyasa
এছাড়াও পড়ুন:
Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar
Gwamna Inuwa ya kuma jaddada bukatar bin ka’idojin kariya a harkokin sufurin ruwa, inda ya yi kira ga shugabannin kananan hukumomi, da shugabannin al’umma, da direbobin kwale-kwale da hukumomin da ke da ruwa da tsaki da sauran wadanda suka dace su kara kaimi wajen ganin ana kiyaye duk ka’idojin kariya don magance sake afkuwar ibtila’in a nan gaba.
Ya umurci Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Jiha (SEMA) da Majalisar. Karamar Hukumar Nafada su bayar da duk wani tallafin da ya dace ga iyalan da abin ya shafa tare da hada hannu da hukumomin da abin ya shafa don inganta tsaro da wayar da kan al’ummomin da ke yankunan kogi.
Gwamna Inuwa Yahaya ya yi addu’a yana mai cewa “A madadin gwamnati da al’ummar Jihar Gombe, ina mika sakon ta’aziyyarmu ga iyalan mamatan tare da addu’ar Allah ya jikansu da rahama ya gafarta musu kurakuransu, ya kuma saka musu da Aljannar Firdaus”.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA