Kwamishina ya yi murabus saboda sauya sheƙar Gwamnan Akwa Ibom
Published: 6th, June 2025 GMT
Kwamishinan Harkoki na Musamman a Jihar Akwa Ibom, Mista Ini Ememobong, ya yi murabus daga muƙaminsa biyo bayan sauya sheƙar Gwamna Umo Eno daga jam’iyyar PDP zuwa APC.
Wannan na zuwa ne bayan gwamnan ya fice daga jam’iyyar PDP zuwa jam’iyyar APC.
Sallah: Gwamna Inuwa ya yi kiran sadaukarwa da haɗin kai Tinubu ba zai canza Kashim a matsayin mataimakinsa ba a 2027 – APCGwamna Eno ya faɗa wa kwamishinoninsa cewa duk wanda ba ya son bin sa zuwa APC ya ajiye aikinsa.
Ememobong, ya ce yana girmama ra’ayin gwamnan, amma ba zai iya binsa APC ba.
“Ba zan iya yin wannan tafiya ba,” in ji Ememobong.
“Na yarda da siyasar aƙida. Na gode wa gwamna bisa ƙauna da ya nuna min, amma dole na tsaya kan abin da nake da yaƙini a kai.”
A ranar Juma’a ne, Gwamna Eno, ya sanar da ficewarsa daga PDP zuwa APC, inda ya ce ya yanke hukuncin ne bayan dogon nazari.
“Na tuntuɓi mutane daga ko ina a cikin jihar,” in ji Eno.
“Wannan shawara ce da ta dace da lokacin da muke ciki. Mun shiga APC ba don mu samu rauni ba, sai don mu ƙara ƙarfi.”
Da wannan sauyin, APC na da iko a jihohi huɗu cikin shida da ke yankin Kudu Maso Gabas, sai Jihohin Ribas da Bayelsa kawai suka rage a hannun PDP.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Akwa Ibom Kwamishina Sauya Sheƙa Siyasa
এছাড়াও পড়ুন:
Tsohon Minista Kabiru Turaki ya zama sabon shugaban PDP na ƙasa
An zaɓi tsohon Ministan Ayyuka na Musamman da Harkokin Gwamnati, Kabiru Tanimu Turaki, a matsayin sabon shugaban Jam’iyyar PDP na ƙasa a yayin babban taron jam’iyyar da aka gudanar a birnin Ibadan na Jihar Oyo a ranar Asabar.
PDP ta ce Barista Kabiru Tanimu Turaki, ya yi nasarar ce akan Sanata Lado Ɗan Marke da ƙuri’u sama da dubu ɗaya da ɗari biyar, da wakilai 3, 131 suka halarta.
PDP za ta sake farɗaɗowa idan shugabanninta suka cire girman kai — Anenih Fintiri ya yi watsi da korar Wike daga PDPHakan dai na zuwa ne yayin da jam’iyyar ta PDP ta dakatar da Wike da wasu jiga-jigan jam’iyyar, yayin da gwamnonin Adamawa da na Fulato suka ƙalubalanci matakin suna masu cewar matakin ka iya ƙara rura wutar rikicin da jam’iyyar ke ciki.
Barista Kabiru Tanimu Turaki, ya samu ƙuri’u 1,516 daga cikin ƙuri’u 1, 834 da aka kaɗa a yayin zaɓen.
A kujeru biyu ne dai aka yi zaɓe a babban taron jam’iyyar na ƙasa, yayin da dama daga sauran kujerun shugabancin jam’iyyar kuma aka yi maslaha a tsakanin ’yan takara wanda daga bisani aka kira wakilai daga jihohi suka kaɗa ƙuri’unsu kamar yadda dokar hukumar zaben Najeriya ta tanada.