A cewarsa, jami’an tsaron sun samu kiran gaggawa da ke cewa, wasu gungun ‘yan fashi da makami sun rufe babbar hanyar, sun fara yin fashi ga matafiya a ranar 4 ga watan Yunin 2025.

 

Nan take aka tura tawaga a ƙarƙashin jagorancin babban jami’in ɗansanda (DPO) da ke kula da caji ofis ɗin Toro, tare da haɗin guiwar sauran jami’an tsaro inda suka nufi wurin da nufin daƙile fashin.

 

Da isarsu wurin, suka fara musayar wuta inda jami’an tsaron suka samu nasarar fatattakarsu wanda hakan ya janyo da dama daga cikin ‘yan fashin suka gamu da raunuka na harbin bindiga sannan an harbe daya ya mutu nan take.

 

LEADERSHIP ta rawaito cewa, an miƙa gawar Shagari ga sashin da ke kula da gawarwaki domin birne shi kamar yadda aka tanada.

 

Wakil ya ƙara da cewa, ana ci gaba da gudanar da bincike domin ganin an bi sawun sauran waɗanda ake zargin ‘yan fashi da makamin ne da suka tsere domin tabbatar da an kamo su.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Guardian: Isra’ila Tana Kai Wa Makarantun Dake Dauke Da ‘Yan Gudun Hijira a gaza Hari, Tana Sane Da Hakan

Jaridar Guardian ta ta kasar Birtaniya ta bada labarin cewa, Hare-haren da sojojin HKI su ka kai kan wata makaranta, inda yan gudun hijira Falasdinawa suke samun mafaka da gangan suka yi shi, suna sane, kuma a halin yanzu suna Shirin kai wa wasu makarantun guda 4 hare-hare nan gaba.

Jaridar ta kara da cewa: Isra’ila ta ayyana wasu Karin makarantu wadanda Falasdinawa suke samun mafaka a cikinsu domin kai musu hare-hare a nan gaba. A lokacinda HKI ta kasa ganin mayakan Hamas a fili sojojinta sun koma kan kissan Falasdinawa fararen hula, wadanda suke samun mafaka a makarantu.

A cikin watanni da suka gabata sojojin mamayar sun kai hare-hare akan wasu gine-ginen 6 wadanda suka kasance makarantu ne, wadanda Falasdinawa maza da mata da yara suka maidasu wuraren fakewa daga hare-haren sojojin HKI, suka kai mutane 120 ga shahada.

A ranar Litinin da ta gabata ce, sojojin mamayar suka kai wani harin a kan makarantar “A’ishiyya” wacce ta zama sansanin ‘yan gudun  hijira a garin Deir-Balah’ na tsakiyar Gaza. Suka kuma kai falasdinawa da dama ga shahada.

Amma suka bada sanarwan cewa, ‘yan ta’adda ne suke fakewa a cikin makarantar, ba tare da sun gabatar da wata shaida ta tabbatar da hakan ba.

 A bisa wani rahoton na MDD ta fitar, ta ce kaso 95% na makarantun Gaza, sun lalace, a yayin da wasu kimani  400 su ka rushe gaba daya saboda hare-haren sojojin yahudawan.  A ranar 26 ga watan Mayu da ya shude ne, sojojin HKI suka kai hare-harei a kan makarantar “Fahmi-Jarjawi” da take cike da ‘yan gudun hijira wanda shi ma ya yi sanadiyyar shahadar Faladinawa da dama.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
  • Sojoji sun dakile hare-haren ‘Yan Boko Haram biyu a Borno
  • Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno
  • An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja
  • Direbobi sun toshe babbar hanyar Kogi sakamakon harbe abokan aikinsu
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato
  • Jami’an DSS sun kashe ’yan bindiga 45 a Neja
  • Gwamnan Katsina Ya Bukaci Hadin Gwiwa Da ‘Yan Kasuwa Domin Cigaban Jihar
  • Guardian: Isra’ila Tana Kai Wa Makarantun Dake Dauke Da ‘Yan Gudun Hijira a gaza Hari, Tana Sane Da Hakan