Direbobi sun toshe babbar hanyar Kogi sakamakon harbe abokan aikinsu
Published: 5th, June 2025 GMT
Wasu direbobin manyan motoci sun rufe hanyar Lokoja zuwa Ajaokuta da ke Jihar Kogi domin nuna fushinsu bayan jami’an tsaro sun harbi ɗaya daga cikinsu da kuma mataimakinsa.
Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne lokacin da jami’an tsaro suka harbi mutanen biyu saboda sun ƙi tsayawa a wajen binciken da aka tsayar da su.
Sai dai, babu wanda ya mutu sakamakon harbin.
An garzaya da su asibiti domin ba su kulawar gaggawa.
Hakan ne, ya sa sauran direbobin suka fusata, suka toshe bakin gadar Ganaja da ke babbar hanyar Lokoja zuwa Ajaokuta.
Sun ƙi ɗauke motocinsu har sai da sojoji suka iso wajen domin kwantar da tarzomar.
Rufe hanyar ta haddasa cunkoso mai yawa, inda matafiya da ma’aikata suka kasa zuwa wuraren aikinsu.
Wasu ma’aikata sun yi tafiya mai nisa a ƙafa, yayin da wasu suka koma gida suka haƙura da zuwa wajen ayyukansu.
Aliyu Dansabe, wani ma’aikaci, ya ce: “Na yi tafiya mai nisa daga rukunin gidaje na Governor Idris Wada har zuwa ofishina, kimanin kilomita bakwai.
“Lamarin ya gajiyar da ni sosai kuma ya tayar min da hankali. Muna godiya da zuwan sojoji da suka shawo kan lamarin.”
Kakakin Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kogi, SP William Aya, ya tabbatar da cewa an shawo kan lamarin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: hanya
এছাড়াও পড়ুন:
Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Aiwatar Da Wani Kisan Kiyashi Kan Masu Bukatar Kayan Agaji
Sojojin mamayar Isra’ilan sun sake aiwatar da wani sabon kisan kiyashi a birnin Rafah, inda suka kashe mutane da dama a kusa da cibiyar rarraba kayan agaji
Fararen hula 23 ne suka yi shahada yayin da wasu kusan 200 suka jikkata a yau Talata lokacin da sojojin mamayar Isra’ila suka bude wuta kan mai uwa da wabi wa fararen hula a kusa da wata cibiyar rarraba kayan agaji a birnin Rafah da ke kudancin Zirin Gaza.
Majiyoyin kiwon lafiya sun bayyana cewa: Shahidan sun fadi ne a lokacin da suke jiran agajin jin kai a titunan Rafah, lokacin da jirage masu saukar ungulu suka bude musu wuta. An tantance biyar daga cikin shahidan, yayin da wasu fiye da 20 kuma har yanzu ba a san ko su waye ba.
Wannan lamari dai ya zo ne a daidai lokacin da ake ci gaba da samun tashe-tashen hankula a yankin, wanda ke nuni da irin mummunan halin jin kai da fararen hula ke fuskanta a zirin Gaza.