Direbobi sun toshe babbar hanyar Kogi sakamakon harbe abokan aikinsu
Published: 5th, June 2025 GMT
Wasu direbobin manyan motoci sun rufe hanyar Lokoja zuwa Ajaokuta da ke Jihar Kogi domin nuna fushinsu bayan jami’an tsaro sun harbi ɗaya daga cikinsu da kuma mataimakinsa.
Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne lokacin da jami’an tsaro suka harbi mutanen biyu saboda sun ƙi tsayawa a wajen binciken da aka tsayar da su.
Sai dai, babu wanda ya mutu sakamakon harbin.
An garzaya da su asibiti domin ba su kulawar gaggawa.
Hakan ne, ya sa sauran direbobin suka fusata, suka toshe bakin gadar Ganaja da ke babbar hanyar Lokoja zuwa Ajaokuta.
Sun ƙi ɗauke motocinsu har sai da sojoji suka iso wajen domin kwantar da tarzomar.
Rufe hanyar ta haddasa cunkoso mai yawa, inda matafiya da ma’aikata suka kasa zuwa wuraren aikinsu.
Wasu ma’aikata sun yi tafiya mai nisa a ƙafa, yayin da wasu suka koma gida suka haƙura da zuwa wajen ayyukansu.
Aliyu Dansabe, wani ma’aikaci, ya ce: “Na yi tafiya mai nisa daga rukunin gidaje na Governor Idris Wada har zuwa ofishina, kimanin kilomita bakwai.
“Lamarin ya gajiyar da ni sosai kuma ya tayar min da hankali. Muna godiya da zuwan sojoji da suka shawo kan lamarin.”
Kakakin Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kogi, SP William Aya, ya tabbatar da cewa an shawo kan lamarin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: hanya
এছাড়াও পড়ুন:
Uwa ta kashe ’ya’yan cikinta biyu saboda kuncin rayuwa
Ana zargin wata uwa a jihar Enugu da kashe ’ya’yanta biyu saboda tsananin kuncin rayuwa.
Lamarin ya faru a unguwar Trans Ekulu da ke yankin birnin na Enugu.
An kone babur din ‘barayin waya’ a Kano Natasha za ta sake komawa kotu kan hana ta shiga harabar majalisaAn ga gawarwakin yara biyu a gidan lokacin da jami’an tsaro sukashiga ciki, lamarin da ya tayar da hankulan jama’ar unguwar.
Yaran da ake zargin uwar tasu da kashewa sun hada da yarinya mai suna Esther Arinze mai shekara hudu da haihuwa da kuma kaninta mai suna Chibusoma.
Ana zargin an yi amfani da makami mai kaifin gaske wajen ji wa yaran raunuka a jikunansu kafin su rasu.
Majiyar labarinmu da rundunar ’yan sandan yankin Trans Ekulu sun amsa kiran gaggawar ne daga unguwar aka shaida musu faruwar lamarin inda su kuma ba su yi kasa a gwiwa ba suka rankaya zuwa gidan inda suka iske gawarwakin yara jina-jina.
Daga bisani dai ’yan sanda sun kwashe gawarwakin yaran zuwa asibitin koyarwa na Jami’ar Jihar Enugu, inda likitoci suka tabbatar da mutuwar su.