Direbobi sun toshe babbar hanyar Kogi sakamakon harbe abokan aikinsu
Published: 5th, June 2025 GMT
Wasu direbobin manyan motoci sun rufe hanyar Lokoja zuwa Ajaokuta da ke Jihar Kogi domin nuna fushinsu bayan jami’an tsaro sun harbi ɗaya daga cikinsu da kuma mataimakinsa.
Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne lokacin da jami’an tsaro suka harbi mutanen biyu saboda sun ƙi tsayawa a wajen binciken da aka tsayar da su.
Sai dai, babu wanda ya mutu sakamakon harbin.
An garzaya da su asibiti domin ba su kulawar gaggawa.
Hakan ne, ya sa sauran direbobin suka fusata, suka toshe bakin gadar Ganaja da ke babbar hanyar Lokoja zuwa Ajaokuta.
Sun ƙi ɗauke motocinsu har sai da sojoji suka iso wajen domin kwantar da tarzomar.
Rufe hanyar ta haddasa cunkoso mai yawa, inda matafiya da ma’aikata suka kasa zuwa wuraren aikinsu.
Wasu ma’aikata sun yi tafiya mai nisa a ƙafa, yayin da wasu suka koma gida suka haƙura da zuwa wajen ayyukansu.
Aliyu Dansabe, wani ma’aikaci, ya ce: “Na yi tafiya mai nisa daga rukunin gidaje na Governor Idris Wada har zuwa ofishina, kimanin kilomita bakwai.
“Lamarin ya gajiyar da ni sosai kuma ya tayar min da hankali. Muna godiya da zuwan sojoji da suka shawo kan lamarin.”
Kakakin Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kogi, SP William Aya, ya tabbatar da cewa an shawo kan lamarin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: hanya
এছাড়াও পড়ুন:
Dan shekara 10 ya kashe mahaifinsa ɗan sanda da bindiga
Wani yaro mai kimanin shekaru goma a duniya ya harbe mahaifinsa wanda jami’in ɗan sanda ne mai mukamin sufeto a Jihar Anambra da ke kudu maso gabashin Nijeriya.
Haka kuma, wakilinmu ya ruwaito cewa yaron ya harbi wani yayansa da bindigar mahaifin nasa ta aiki kirar AK-47.
Kashe jagoran addini na Iran zai kawo ƙarshen yaƙi — Netanyahu Mun bankaɗo sabuwar dabarar ’yan siyasa ta satar kuɗi — EFCCWannan dai na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ’yan sandan Anambra, Tochukwu Ikenga ya raba wa manema labarai a ranar Litinin.
Kakakin ya ce an gaggauta kai jamin asibiti domin a ceto rayuwarsa amma likitoci suka tabbatar da cewa rai ya riga ya yi halinsa.
Sanarwar ta ce “a ranar Lahadi 15 ga watan Yuni, dan gidan wani jami’in dan sanda mai kimanin shekara goma da haihuwa ya harbe mahaifinsa har lahira ya kuma jiwa yayan sa mummunan rauni.
“Abin bakin ciki muna sanar da ku mutuwar jami’inmu mai mukamin sufeto, Okolie Amechi, bisa harbe shi da dansa ya yi a gidansa.
“Wannan ba karamin abin takaici ba ne da kaddara,” in ji sanarwar.