Aminiya:
2025-06-06@07:28:56 GMT

Kotu ta aike da ɗan Tiktok gidan yari kan yin shigar mata a Kano

Published: 4th, June 2025 GMT

Wata kotu da ke unguwar Noman’s Land a Jihar Kano, ta bayar da umarnin tsare fitaccen ɗan TikTok, Abubakar Kilina, a gidan gyaran hali har zuwa ranar 17 ga Yuni, 2025.

Wannan hukunci ya biyo bayan tuhumar da Hukumar Tace Fina-Finai da Ɗab’i ta Jihar Kano, ta shigar da ke zargin sa da aikata halaye da suka saɓa wa tarbiyya da al’adu Hausawa.

Sallah: Mun shirya samar da tsaro a Yobe — ’Yan Sanda Ba zan yi musayar yawu da yara ba — Martanin Amaechi ga Wike

Shugaban hukumar, Abba El-Mustapha, ya bayyana cewa wannan mataki wani ɓangare ne na yunƙurin hukumar na daƙile yaɗuwar rashin ɗa’a a kafafen sada zumunta, musamman TikTok.

“Mun ƙudiri aniyar daƙile duk wani abin da zai ci karo da tarbiyya da koyarwar addinin Musulunci a Kano.

“Wannan matakin kotu yana nuna cewa ba za mu lamunci irin wannan hali daga matasa ba,” in ji Abba.

Mai shari’a Hajiya Halima Wali, wacce ta jagoranci zaman kotun, ta bayar da umarnin tsare Abubakar Kilina har zuwa ranar da za a ci gaba da sauraron ƙarar, bayan ya amsa dukkanin tuhume-tuhumen da aka karanta masa.

“Laifin da ake tuhumarsa da shi ya saɓa da doka, kuma ya amsa laifinsa kai tsaye. Dole ne mu ɗauki matakin da ya dace don hakan ya zama izina ga wasu,” cewar wata majiya daga kotun.

A cewar hukumar, ana zargin Kilina da yin shigar mata da kuma yin kalamai na nuna rashin tarbiyya a shafinsa na TikTok, wanda hakan ke kawo rashin ɗa’a da kuma tasiri mara kyau ga matasa.

“Mun daɗe muna faɗakarwa da gargaɗi. Amma yanzu lokaci ya yi da za mu ɗauki matakin doka domin dakatar da wannan mummunan lamari,” in ji Abdullahi Sani Sulaiman, jami’in yaɗa labarai na hukumar.

Hukumar tace fina-finai ta Kano ta ce wannan ba shi ne karon farko ba da ta ke kai matasa gaban kotu a kan irin waɗannan halaye.

A baya an samu wasu da aka yanke wa hukuncin ɗaurin shekara ɗaya ko zaɓin biyan tarar Naira 100,000 tare da sharaɗin ka da su ƙara maimaita irin wannan laifi.

“Wannan yunƙuri namu yana nufin kare martabar Kano da al’adunta daga shigowar ɗabi’un da ba su dace ba, musamman a kafafen sada zumunta,” in ji Abba.

Alƙalin ta ɗage sauraron shari’ar zuwa 17 ga watan Yuni, 2025, domin yanke hukunci.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Abubakar Kilina ɗauri Gidan Yari Hukumar Tace Fina Finai Shigar mata

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Yadda Mayar Da Unguwa Mayanka Ke Shafar Lafiyar Al’umma

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Wata al’ada da ta zama gama gari a tsakanin matasa, ita ce yankewa da fige kaji a unguwanni, musamman a lokutan bukukuwan Sallah.

A da, ana da wurare na musamman da ake yin irin wannan abu.

NAJERIYA A YAU: Hanyoyin kauce wa ɓarnar ambaliyar ruwa NAJERIYA A YAU: Mokwa: Tsakanin Taraddadin Rashin Matsuguni Da Jimamin Rashin ’Yan-Uwa

Sai dai masana sun ce wannan abu na iya haifar da matsaloli ga lafiya da kuma gurɓata muhalli.

Wannan shi ne abin da shirin Najeriya A Yau zai tattauna a kai, yayin da ake Bikin Ranar Muhalli ta Duniya kwana ɗaya kafin Babbar Sallah.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mun gurfanar da mutum 29 a kotu kan zargin kashe DPO a Kano – ’Yan sanda
  • Bukukuwan sallah tare da Malta Guinness a Birnin Kano
  • Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore
  • Sakon Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ga Mahajjatan Aikin Hajjin Bana A Kasa Mai Tsarki
  • PDP ce kaɗai jam’iyyar adawa mai ƙarfi a Najeriya — Saraki
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Mayar Da Unguwa Mayanka Ke Shafar Lafiyar Al’umma
  • Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano
  • Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 
  • Mali: Kotu Ta Yi Watsi Da Neman Dage Haramcin Da Aka Yi Wa Jam’iyyun Siyasar Kasar