Aminiya:
2025-11-03@01:59:27 GMT

Kotu ta aike da ɗan Tiktok gidan yari kan yin shigar mata a Kano

Published: 4th, June 2025 GMT

Wata kotu da ke unguwar Noman’s Land a Jihar Kano, ta bayar da umarnin tsare fitaccen ɗan TikTok, Abubakar Kilina, a gidan gyaran hali har zuwa ranar 17 ga Yuni, 2025.

Wannan hukunci ya biyo bayan tuhumar da Hukumar Tace Fina-Finai da Ɗab’i ta Jihar Kano, ta shigar da ke zargin sa da aikata halaye da suka saɓa wa tarbiyya da al’adu Hausawa.

Sallah: Mun shirya samar da tsaro a Yobe — ’Yan Sanda Ba zan yi musayar yawu da yara ba — Martanin Amaechi ga Wike

Shugaban hukumar, Abba El-Mustapha, ya bayyana cewa wannan mataki wani ɓangare ne na yunƙurin hukumar na daƙile yaɗuwar rashin ɗa’a a kafafen sada zumunta, musamman TikTok.

“Mun ƙudiri aniyar daƙile duk wani abin da zai ci karo da tarbiyya da koyarwar addinin Musulunci a Kano.

“Wannan matakin kotu yana nuna cewa ba za mu lamunci irin wannan hali daga matasa ba,” in ji Abba.

Mai shari’a Hajiya Halima Wali, wacce ta jagoranci zaman kotun, ta bayar da umarnin tsare Abubakar Kilina har zuwa ranar da za a ci gaba da sauraron ƙarar, bayan ya amsa dukkanin tuhume-tuhumen da aka karanta masa.

“Laifin da ake tuhumarsa da shi ya saɓa da doka, kuma ya amsa laifinsa kai tsaye. Dole ne mu ɗauki matakin da ya dace don hakan ya zama izina ga wasu,” cewar wata majiya daga kotun.

A cewar hukumar, ana zargin Kilina da yin shigar mata da kuma yin kalamai na nuna rashin tarbiyya a shafinsa na TikTok, wanda hakan ke kawo rashin ɗa’a da kuma tasiri mara kyau ga matasa.

“Mun daɗe muna faɗakarwa da gargaɗi. Amma yanzu lokaci ya yi da za mu ɗauki matakin doka domin dakatar da wannan mummunan lamari,” in ji Abdullahi Sani Sulaiman, jami’in yaɗa labarai na hukumar.

Hukumar tace fina-finai ta Kano ta ce wannan ba shi ne karon farko ba da ta ke kai matasa gaban kotu a kan irin waɗannan halaye.

A baya an samu wasu da aka yanke wa hukuncin ɗaurin shekara ɗaya ko zaɓin biyan tarar Naira 100,000 tare da sharaɗin ka da su ƙara maimaita irin wannan laifi.

“Wannan yunƙuri namu yana nufin kare martabar Kano da al’adunta daga shigowar ɗabi’un da ba su dace ba, musamman a kafafen sada zumunta,” in ji Abba.

Alƙalin ta ɗage sauraron shari’ar zuwa 17 ga watan Yuni, 2025, domin yanke hukunci.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Abubakar Kilina ɗauri Gidan Yari Hukumar Tace Fina Finai Shigar mata

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar

Daga Usman Muhammad Zaria 

 

Majalisar Zartarwa ta Jihar Jigawa ta amince da bayar da rancen kudi ga hukumar gidaje ta jihar domin gina gidaje 52 a Dutse.

A cikin wata sanarwa da kwamishinan yada labarai na jihar, Alhaji Sagir Musa Ahmed ya fitar, ya bayyana cewa gidajen za su kunshi masu dakuna uku da kuma dakuna biyu kowanne.

Ya ce aikin zai kasance a gaban tsohuwar unguwar majalisar dokoki, kusa da hanyar wucewa ta Jami’ar Tarayya da je Dutse, a matsayin wani shiri na asusun gina gidaje karkashin ma’aikatar gidaje, ci gaban birane da tsare-tsaren yankuna, ta hannun hukumar gidaje ta jihar.

Alhaji Sagir ya bayyana cewa, wannan mataki na nuna kudirin gwamnati wajen magance matsalar gidaje a babban birnin jihar, kara habaka ci gaban birane, tare da samar da ayyukan yi ga matasan jihar.

Ya ce an tsara wannan asusu  ne domin tabbatar da dorewa, ta yadda za a ci gaba da zuba jari a ayyukan samar da gidaje masu araha a fadin jihar.

Haka kuma ya kara da cewa, gwamnatin jihar tana da kudirin ci gaba da inganta rayuwar al’ummarta, ta hanyar ayyuka masu amfani da jama’a, da ke inganta walwala, karfafa tattalin arziki, da tallafa wa matasa.

Kwamishinan ya kuma bayyana cewa, majalisar ta amince da bayar da kwangilar gyara da inganta gidan baki guda biyu (Malam Adamu Chiroma House da kuma Senator Francis Ella House) da ke cikin G9 Quarters a Dutse, da kudin sama da naira miliyan 219.7.

Ya ce aikin zai haɗa da cikakken gyara da inganta gine-ginen, gyaran hanyoyin ruwa da kuma girka tankokin  ruwa ga kowanne daga cikin gidajen biyu.

Ya ce hakan na da nufin tabbatar da wadataccen ruwan sha mai dorewa a  wuraren.

Alhaji Sagir Musa Ahmed ya kara da cewa, amincewar da aka yi da wannan kwangila na nuna jajircewar gwamnatin jihar wajen kula da dukiyar jama’a da kuma tabbatar da cewa gine-ginen gwamnati suna cikin yanayi mai kyau da nagarta.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fursunan da aka yanke wa hukuncin kisa ya tsere daga gidan yari a Yobe
  • Tinubu ya yanke hulɗa da Amurka kawai — Sheikh Gumi
  • Dan Majalisar Jema’a/Sanga, Daniel Amos, Ya Koma Jam’iyyar APC
  • Kofin kofi mafi tsada a duniya ya shiga kasuwa a kan Naira miliyan 1.5m
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Kotu ta dakatar da gudanar da babban taron PDP
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Kotu ta dakatar da babban taron PDP na ƙasa
  • Kotu ta dakatar da babban taron PDP
  • Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC