Aminiya:
2025-09-18@02:19:29 GMT

Kotu ta aike da ɗan Tiktok gidan yari kan yin shigar mata a Kano

Published: 4th, June 2025 GMT

Wata kotu da ke unguwar Noman’s Land a Jihar Kano, ta bayar da umarnin tsare fitaccen ɗan TikTok, Abubakar Kilina, a gidan gyaran hali har zuwa ranar 17 ga Yuni, 2025.

Wannan hukunci ya biyo bayan tuhumar da Hukumar Tace Fina-Finai da Ɗab’i ta Jihar Kano, ta shigar da ke zargin sa da aikata halaye da suka saɓa wa tarbiyya da al’adu Hausawa.

Sallah: Mun shirya samar da tsaro a Yobe — ’Yan Sanda Ba zan yi musayar yawu da yara ba — Martanin Amaechi ga Wike

Shugaban hukumar, Abba El-Mustapha, ya bayyana cewa wannan mataki wani ɓangare ne na yunƙurin hukumar na daƙile yaɗuwar rashin ɗa’a a kafafen sada zumunta, musamman TikTok.

“Mun ƙudiri aniyar daƙile duk wani abin da zai ci karo da tarbiyya da koyarwar addinin Musulunci a Kano.

“Wannan matakin kotu yana nuna cewa ba za mu lamunci irin wannan hali daga matasa ba,” in ji Abba.

Mai shari’a Hajiya Halima Wali, wacce ta jagoranci zaman kotun, ta bayar da umarnin tsare Abubakar Kilina har zuwa ranar da za a ci gaba da sauraron ƙarar, bayan ya amsa dukkanin tuhume-tuhumen da aka karanta masa.

“Laifin da ake tuhumarsa da shi ya saɓa da doka, kuma ya amsa laifinsa kai tsaye. Dole ne mu ɗauki matakin da ya dace don hakan ya zama izina ga wasu,” cewar wata majiya daga kotun.

A cewar hukumar, ana zargin Kilina da yin shigar mata da kuma yin kalamai na nuna rashin tarbiyya a shafinsa na TikTok, wanda hakan ke kawo rashin ɗa’a da kuma tasiri mara kyau ga matasa.

“Mun daɗe muna faɗakarwa da gargaɗi. Amma yanzu lokaci ya yi da za mu ɗauki matakin doka domin dakatar da wannan mummunan lamari,” in ji Abdullahi Sani Sulaiman, jami’in yaɗa labarai na hukumar.

Hukumar tace fina-finai ta Kano ta ce wannan ba shi ne karon farko ba da ta ke kai matasa gaban kotu a kan irin waɗannan halaye.

A baya an samu wasu da aka yanke wa hukuncin ɗaurin shekara ɗaya ko zaɓin biyan tarar Naira 100,000 tare da sharaɗin ka da su ƙara maimaita irin wannan laifi.

“Wannan yunƙuri namu yana nufin kare martabar Kano da al’adunta daga shigowar ɗabi’un da ba su dace ba, musamman a kafafen sada zumunta,” in ji Abba.

Alƙalin ta ɗage sauraron shari’ar zuwa 17 ga watan Yuni, 2025, domin yanke hukunci.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Abubakar Kilina ɗauri Gidan Yari Hukumar Tace Fina Finai Shigar mata

এছাড়াও পড়ুন:

Microsoft ya ƙwace shafukan wasu kamfanoni 340 a Najeriya

Kamfanin Microsoft ya sanar da ƙwace shafukan yanar gizo na wasu kamfanoni 340 a Najeriya bayan samunsu da laifin sarrafa fasahohin kamfanin ba bisa ƙa’ida ba, musamman satar bayanan mutane.

Sanarwar da Microsoft ya fitar ta ce matakin ya biyo bayan wani umarni da wata kotu a Amurka ta bayar tun a farkon wannan wata, wadda ta bai wa kamfanin damar ɗaukar matakin ladabtarwa ga waɗanda ke amfani da fasaharsa ba tare da izini ba.

An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe

Steven Masada, mataimakin shugaban sashen lauyoyi na Microsoft da ke kula da laifukan intanet, ya bayyana cewa waɗannan kamfanoni sun ɗauki bayanan abokan hulɗarsu sama da 5,000, inda suka yi amfani da shafukan kutse domin samun bayanan sirri.

A cewarsa, ɗaya daga cikin shafukan da suka fi haddasa damuwa shi ne wani da ake kira Raccoon0356, wanda ke da mabiya fiye da 850 a manhajar Telegram. Wannan shafi ne ke bai wa wasu damar samun kayan aikin kutse don shigar bayanan sirri na Microsoft da wasu hukumomi.

Microsoft ya bayyyana Joshua Ogundipe, mazaunin Najeriya a matsayin wanda ke jagorantar wannan shafi da ke kan manhajar Telegram, kuma bai bayar da amsa a saƙon da aka aike masa ba, don ya kare kanshi game da ayyukan da kamfanin ya ce yana aikatawa.

Kamfanin na Microsoft ya ce ya gano yadda Joshua ya jima tare da ƙwarewa wajen satar bayanan mutane, inda a tsakanin 12 zuwa 28 ga watan Fabrairun wannan shekara, ya yi kutse a shafukan hukumomi sama da 2,300, mafi yawansu na Amurka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare
  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Microsoft ya ƙwace shafukan wasu kamfanoni 340 a Najeriya
  • Karamar Hukumar Birnin Kano Ta Kaddamar Da Kula Da Lafiyar Ido Kyauta
  • Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi
  • Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
  • DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu
  • DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu