Jirgin soji ya kashe mutane 20 a Zamfara
Published: 2nd, June 2025 GMT
Aƙalla mutane 20 ne suka mutu bayan wani hari da jiragen sama na sojojin Najeriya (NAF) ya kai domin fatattakar ’yan bindiga a a Jihar Zamfara.
Jiragen sojin sun kashe wasu ’yan sa-kai bisa kuskure, a yayin da ’yan sa-kan suke ƙoƙarin fatattakar ’yan bindiga da suka kai hari a yankin Mani a Ƙaramar Hukumar Maru.
Jiragen sojin sun kai hare-haren ne domin fatattakar ’yan bindiga da suka kai wa manoma hari a kan babura da rana tsaka.
Mazauna yankin sun ce bayan ’yan bindiga sun sace manoma sama da 50 ne jirgin sojin ya amsa kiran gaggawa, amma aka samu kuskure ya kashe wasu ’yan sa-kai da ke ƙoƙarin fatattakar maharan.
Bom ɗin Boko Haram ya kashe fasinjoji 9 a tashar mota a Borno NAJERIYA A YAU: Mokwa: Tsakanin Taraddadin Rashin Matsuguni Da Jimamin Rashin ’Yan-UwaWani mazaunin yankin ya shaida wa kafar BBC cewa, “Mun sanar da jami’an tsaro bayan harin, amma kawai sai muka ga jirgin ya zo ya kashe ’yan sa-kai na mu.”
Wani mazaunin garin ya ce, a yayin da jama’a ke ƙoƙarin taimaka wa wadanda aka kai wa hari, sai ga wani jirgin saman soji ya iso.
Ya ce, “’Yan bindigar sun tafi da mutane 50, amma yayin da muke ƙoƙarin kai ɗauki, sai muka ga jirgin soji, kuma ya fara harbin mu. Kowa ya gudu neman mafaka,” inda ya ƙara da cewa sun yi kamar matattu ne don su tsira.
Wani mazaunin kuma ya yi kira ga jami’an tsaro da su ƙara yawa, inda ya buƙaci a yankin amma su yi taka-tsantsan yayin gudanar da ayyukan.
Har yanzu sojojin Najeriya ba su ce komai ba game da lamarin.
Idan ba a manta ba, ire-iren wannan harin huskure ya faru a baya a yankin Jihar Zamfara. A watan Janairun 2025, wani harin jirgin saman sojin Najeriya ya kashe mutane 16 bisa kuskure, ciki har da ’yan sa-kai da manoma, a ƙauyen Tungar Kara a Jihar Zamfara, bayan an zaci su ’yan bindiga ne.
Hakazalika, a watan Disambar 2024, wani harin jirgin sama a Jihar Sakkwato ya kashe fararen hula 10 a sakamakon abin da Gwamnan jihar ya bayyana a matsayin harin kuskure kan fararen hula.
A watan Disamban shekarar 2023 wani jirgin soja ya kai irin harin inda ya kashe sama da fararen hula kimanin 100 a wurin taron Mauludi a yankin Tudun Biri da ke Ƙaramar Hukumar Igabi a Jihar Kaduna.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
Bom ɗin Boko Haram ya kashe fasinjoji 9 a tashar mota a Borno
Mutane tara sun mutu wasu da dama sun jikkata sakamakon tashin wani abu mai fashewa da ’yan Boko Haram suka dasa a ƙauyen Mairari da ke Ƙaramar Hukumar Guzamala ta Jihar Borno.
Lamarin ya faru a wata tashar mota a kauyen, wanda ke da nisan kilomita 18 daga Karamar Hukumar Monguno da kuma kilomita 119 daga Maiduguri.
Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Borno, Abdulkarim Lawan, mai wakiltar yankin, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana shi a matsayin “rashin imani.”
Abdulkarim Lawal ya bayyana cewa waɗanda lamarin ya shafa mazauna yankin ne masu juriya da ke komawa gonakinsu a Mairari.
NAJERIYA A YAU: Mokwa: Tsakanin Taraddadin Rashin Matsuguni Da Jimamin Rashin ’Yan-Uwa Layya da hukunce-hukuncenta a MusulunciKafin yanzu, sau biyu ana sake tsugunar da mutanen yankin bayan sun yi gudun hijira, amma hare-haren Boko Haram na sake tilasta musu yin ƙaura.
Lawan ya yi kira ga sojoji da su ƙaddamar da ayyuka masu zafi domin ƙwato ɗauƙacin Ƙaramar Hukumar Guzamala, ciki har da Gudumbali da Mairari, waɗanda ya ce suna ƙarƙashin ikon ’yan ta’adda.
Shugaban majalisar ya ce, “Abin takaici ne yadda mutane tara daga cikin al’ummata masu juriya suka mutu sakamakon fashewar bom da aka dasa yayin da suke jiran shiga motocin haya a wata tashar mota a kauyen Mairari.”
Ya addu’ar samu rahama ga mamatan da kuma samun lafiya ga wadanda suka jikkata.
Ya yaba da ƙoƙarin sabon Kwamandan rundunar Operation Hadin Kai, Manjo-Janar Abdulsalam Abubakar, amma ya sake jaddada buƙatar gaggawa ta dawo da mulkin farar hula a yankunan da abin ya shafa.
A sauya wa Barikin Giwa wuri — Kungiyar Bale GaltimariA wani labarin mai nasaba da hakan, Ƙungiyar Tuntuɓa ta Bale Galtimari ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta kawar da barikin sojoji na Giwa daga inda yake a Maiduguri.
Dakta Zanna Boguma, shugaban kungiyar, ya bayyana yadda Boko Haram ke kai hare-hare akai-akai ga barikin, lamarin da ke jefa rayuwar mazauna yankin fiye da miliyan daya cikin hadari a yankunan farar hula kamar Galtimari, Fori, da 122.
Ya lura cewa barikin, wanda ake kyautata zaton yana tsare da ’yan ta’adda, an kai masa hari akai-akai domin sakin su, a 2014, 2015 (sau uku), da 2019.
Ƙungiyar ta jaddada cewa bai kamata a gina manyan sansanonin sojoji a cikin al’ummomin farar hula ba.