HausaTv:
2025-07-24@03:25:01 GMT

 Iran  Ce Ta Farko A Duniya Wajen Dashen Koda

Published: 1st, June 2025 GMT

Mataimakin shugaban kungiyar Iraniyawa masu bayar da kyautar gabban jikinsu ga mabukata, Umid Qabadi, ya bayyana cewa; A cikin shekaru 25 da su ka gabata, yadda ake kyautar gabban jiki domin yin dashe a duniya ya karu da kaso 70%, kuma Iran ce ta farko wajen yin dashen koda, har ma ana yi ma ta kirari da; Sarauniyar dashen koda.

A yayin wani taro na girmama masu bayar da kyautar gabban jikin nasu domin yi dashe ga mabukata a gundunar Qazwin, mataimakin shugaban kungiyar Umid Qabadi ya ce; Iran ce ta farko a duniya wajen yin dashen gabobi ga marasa lafiya mabukata.

Qabadi ya yi ishara da wajabci ganin an bunkasa wannan al’ada ta bayar da gabobin jiki domin yin dashe saboda a ceto da rayukar mutane, yana mai kara da cewa; A gundumar Qazawin a shekarar da ta gabata, mutane 12 sun bayar da kyautar gabobin jikinsu ga mabukata. Amma a cikin watanni biyu na wannan shekarar kadai, an sami mutane bakwai da su ka bayar da kyautar gabobin jikin nasu ga mabukata.”

Har ila yau, mataimakin shugaban kungiyar masu bayar da gabobin jikin nasu ga mabukata ya ambaci cewa; An kafa wani tsari a Iran na yin jigila ta sama ta marasa lafiya da suke da bukatar a yi musu dashe, zuwa wasu gundumomi na kasar.

Qabadi ya ambaci cewa; A shekarar 1989 ne wanda ya assasa jamhuriyar musulunci ta Iran, Imam Khumaini ( QS) ya bayar da fatawar halarta bayar da gabobin jiki domin ceto da marasa lafiya mabukata, daga wadanda su ka rasu ta hanyar bugun kwakwalwa.” Qabani ya bayyana wanann fatawar a matsayin daya daga cikin muhimman ci gaban da juyin musulunci ya samar.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: bayar da kyautar

এছাড়াও পড়ুন:

Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Jaddada Hakkinta Na Tace Sinadarin Uranium A Cikin Kasarta

Ministan harkokin wajen kasar Iran ya jaddada cewa; Ba zai yiwu Iran ta iya yin watsi da shirinta na inganta sinadarin Uranium ba

Ministan harkokin wajen kasar Iran ya jaddada cewa: Har yanzu ba a daina sarrafa sinadarin Uranium ba a Iran, duk da irin barnar da hare-haren Amurka ya yi wa cibiyoyin makamashin nukiliyar Iran.

A wata hirarsa da Fox News, Araqchi ya amsa tambayoyi kan cewa: “Shin shirin inganta sinadarin Uranium a Iran ya dawo? Shin har yanzu yana ci gaba, ko kuma barnar da aka yi wa Iran ya yi tsanani har ta kai ga dakatar da shi gaba daya?” Araqchi ya amsa da cewa; “Ba a daina bainganta sinadarin ba, duk da cewa barnar ta yi tsanani, amma duniya ta sani Iran ba za ta iya yin watsi da shirinta na inganta sinadarin Uranium ba saboda muhimmancinsa, domin wannan nasara ce ta masana kimiyyar kasar, kuma a halin yanzu abin alfahari ne ga kasa, kuma inganta sinadarin Uranium yana da matukar muhimmanci ga Iran.”

Da yake amsa tambayar cewa: “Mene ne dalilin da ya sa Iran ba za ta shigo da sinadarin uranium da ake inganta shi daga waje ba kamar yadda wasu kasashe ke yi? Araqchi ya ce: “Saboda wannan nasara ce ta ilimi, nasara ce da kasar Iran ta samu, to me ya sa za mu shigo da shi daga waje, duk da za ta iya samar da kanta?”.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Jaddada Hakkinta Na Tace Sinadarin Uranium A Cikin Kasarta
  • Sheikh Qasem: Nuna Halin Ko In-Kula Na Duniya Ne Ya Jawo Kisan Kiyashi A Gaza
  • Taron Kolin Sin Da EU Zai Bayar Da Damar Zurfafa Hadin Gwiwar Sassan Biyu
  • Majalisar Dattawa ta sahale wa Tinubu karɓo rancen $21bn a ƙetare
  • Karin Maganar Sinawa: Koyar Da Su Ya Fi Bayar Da Kifi
  • Sin Ta Samar Da Karin Guraben Aikin Yi Miliyan 6.95 A Rabin Farko Na Bana
  • Hukumar Kashe Gobara Ta Jihar Kwara Ta Taimaka Wajen Hana Lalacewar Wani Bene A Ilorin
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce; Iran Ba Zata Bar Tace Sinadarin Uranium Ba
  • Jami’in Shari’ar Kasa Da Kasa Ya Bayyana Cewa: Harin Da Aka kai Kan Iran Babban Laifi Ne
  • Birgediya Janar Sabahi Fard Ya Jaddada Cewa: Duk Wani Sabon Hari Kan Iran Zai Fuskanci Martani Mai Gauni