HausaTv:
2025-06-03@10:51:18 GMT

 Iran  Ce Ta Farko A Duniya Wajen Dashen Koda

Published: 1st, June 2025 GMT

Mataimakin shugaban kungiyar Iraniyawa masu bayar da kyautar gabban jikinsu ga mabukata, Umid Qabadi, ya bayyana cewa; A cikin shekaru 25 da su ka gabata, yadda ake kyautar gabban jiki domin yin dashe a duniya ya karu da kaso 70%, kuma Iran ce ta farko wajen yin dashen koda, har ma ana yi ma ta kirari da; Sarauniyar dashen koda.

A yayin wani taro na girmama masu bayar da kyautar gabban jikin nasu domin yi dashe ga mabukata a gundunar Qazwin, mataimakin shugaban kungiyar Umid Qabadi ya ce; Iran ce ta farko a duniya wajen yin dashen gabobi ga marasa lafiya mabukata.

Qabadi ya yi ishara da wajabci ganin an bunkasa wannan al’ada ta bayar da gabobin jiki domin yin dashe saboda a ceto da rayukar mutane, yana mai kara da cewa; A gundumar Qazawin a shekarar da ta gabata, mutane 12 sun bayar da kyautar gabobin jikinsu ga mabukata. Amma a cikin watanni biyu na wannan shekarar kadai, an sami mutane bakwai da su ka bayar da kyautar gabobin jikin nasu ga mabukata.”

Har ila yau, mataimakin shugaban kungiyar masu bayar da gabobin jikin nasu ga mabukata ya ambaci cewa; An kafa wani tsari a Iran na yin jigila ta sama ta marasa lafiya da suke da bukatar a yi musu dashe, zuwa wasu gundumomi na kasar.

Qabadi ya ambaci cewa; A shekarar 1989 ne wanda ya assasa jamhuriyar musulunci ta Iran, Imam Khumaini ( QS) ya bayar da fatawar halarta bayar da gabobin jiki domin ceto da marasa lafiya mabukata, daga wadanda su ka rasu ta hanyar bugun kwakwalwa.” Qabani ya bayyana wanann fatawar a matsayin daya daga cikin muhimman ci gaban da juyin musulunci ya samar.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: bayar da kyautar

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Iran Ta Soki Rahoton Hukumar IAEA Na Baya-Bayan Nan Shirinta Na Makamashin Nukiliya

Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ta bayyana cewa: Rahoton IAEA na nuna son kai kuma an shirya shi ne a karkashin tasirin wasu kasashe

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa: Rahoton da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya ta fitar ya kunshi maimaici da wuce gona da iri, yana mai jaddada cewa, an shirya wannan rahoton ne karkashin tasirin wasu kasashen Turai. Ya bayyana takaicinsa kan yadda kasashen yammacin duniya ke cutar da martabar wata kungiya ta duniya ta hanyar siyasantar da ayyukanta.

A farkon taron manema labarai na mako-mako, Baghaei ya yi la’akari da zagayowar ranar wafatin Imam Khumaini (Allah ya kara masa yarda) da shahidan juyin juya halin Musulunci. Ya kara da cewa: Ma’aikatar harkokin wajen kasar na ci gaba da gudanar da ayyukanta na bin diddigin batutuwan da suka shafi diflomasiyya, yana mai nuni da ziyarar da ministan harkokin wajen Iran ke yi a kasar Masar a halin yanzu, da ziyarar da zai kai kasar Lebanon gobe, da kuma gajeriyar ziyarar ministan harkokin wajen kasar Oman a birnin Tehran. Ya kuma bayyana ziyarar da mataimakin shugaban kasar Iran na farko ya kai kasar Tajikistan domin halartar taron kasa da kasa, da kuma ziyarar shugaban majalisar shawarar Musulunci ta Iran yake yi a kasashen Latin Amurka, inda ya jaddada cewa ayyukan sun hada da batun abubuwan dasuka shafi kasashen da na kasa da kasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Arakci: Cinikayya A Tsakanin Iran Da Masar Za Ta Kara Bunkasa
  • Iran Ta Bayar Da Shawarar Kafa Bankin Hadin Gwiwa Na Kasashen Kungiyar Shangai
  • Kasar Iran Ta Soki Rahoton Hukumar IAEA Na Baya-Bayan Nan Shirinta Na Makamashin Nukiliya
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Tattauna Darakta-Janar Na Hukumar Kula Da Makamashin Nukiliya Ta Duniya
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Gargadi Hukumar Kula Da Makamashin Nukiliya Ta Duniya Da Wasu Kasashe
  • ECOWAS Da CORET Sun Shirya Taro Domin Cigaban Makarantun Fulani A Kaduna
  • An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya
  • Iran Ta Kaddamarda Sabbin Magunguna Har 23 Tare Riga Kafin HPV A Karon Farko A Kasar
  • Indiya ta amsa cewa Pakistan ta kakkaɓo jiragen yaƙinta