ECOWAS Da CORET Sun Shirya Taro Domin Cigaban Makarantun Fulani A Kaduna
Published: 1st, June 2025 GMT
Kungiyar Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afrika ECOWAS, tare da haɗin gwiwar Kungiyar Haɗin Kan Masu Kiwon Gargajiya ta Afrika CORET, ta shirya taron horaswa domin ƙarfafa fahimta kan tsarin ciyar da ɗalibai a makarantu, musamman a cikin al’ummomin makiyaya a Jihar Kaduna.
Da yake ƙaddamar da taron a Ladugga, cikin Karamar Hukumar Kachia ta Jihar Kaduna, Ko’odinetan Shirin na CORET, Dr.
Wannan shiri, wanda ke samun goyon bayan haɗin gwiwa daga Swiss Cooperation, na nufin tallafa wa makarantun Fulani da ke Ladugga a Kaduna da kuma Maigatari a Jihar Jigawa, inda ita kuma CORET ke zama jagorar aiwatar da shirin a jihohin biyu.
Ko’odinetan Shirin, Dr. Abdu Umar Ardo ya ce horon yana da nufin ƙarfafa ƙwarewar Kwamitocin Gudanar da Makarantu (SBMC), Ƙungiyoyin Iyaye Mata da na PTA, domin tallafa wa ilimin ‘ya’ya mata da rage yawan yaran da ke zaman gida ba tare da zuwa makaranta ba, musamman a cikin al’ummomin makiyaya.
Dr Ardo wanda ya samu wakilincin Baban Jami’in Sa Ido da Kimantawa na CORET, Alhaji Bimbi Adamu Tahir, ya shawarci mahalarta taron su yi amfani da ilimin da suka samu domin amfanar da al’ummominsu.
A nata jawabin, Shugabar Ƙungiyar Reube Fulbe Development Rights Initiative, Hajiya Halima Yoman, ta jaddada muhimmancin haɗa Ƙungiyoyin Iyaye Mata da Kwamitocin Gudanarwar Makarantu domin kara yawan yaya mata a makarantu.
Ta ce hakan zai taimaka wajen shawo kan matsalar ƙarancin halartar ‘ya’ya mata a makarantun Fulani, tana mai cewa “Ilmantar da mace kamar ilmantar da gaba ɗaya al’umma ne.”
A nata jawabin, Wakiliyar Hukumar Ba da Ilimin Bai Ɗaya ta Jihar Kaduna (SUBEB), Hajiya Hauwa’u Muhammad, ta yi karin bayani game da aikin Kwamitin kula da makarantu kamar haka.
“Kwamitocin Gudanar da Makarantu suna zama hanyar sadarwa tsakanin makaranta da al’umma, inda suke ƙarfafa shiga tsakanin iyaye da shugabannin al’umma da ƙungiyoyi na cikin gida wajen gudanar da harkokin makaranta.”
“Suna kuma marawa baya shigar ‘ya’ya mata da sauran marasa galihu makaranta, ta hanyar warware matsalolin al’ada da na zamantakewa da ke hana su halarta.”
“Kwamitocin na taimakawa wajen sa ido kan ingancin koyarwa da karatun ɗalibai da malamai, domin tabbatar da gaskiya da inganci a harkar ilimi.”
Wasu daga cikin mahalarta taron da suka yi magana da Radio Nigeria Kaduna sun nuna farin cikinsu, inda suka bayyana taron a matsayin mai matuƙar amfani kuma daidai lokacin da ake bukata.
Sun kuma tabbatar wa CORET cewa za su yi amfani da ilimin da suka samu wajen inganta halartar makaranta da gudanar da ita a al’ummominsu.
Taron ya mayar da hankali ne kan manyan al’ummomin Fulani guda uku da ke Ladugga a Kachia: Wuro Nyako da Mbela Biradam da kuma Tiggirde.
COV: Adamu Yusuf
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: ECOWAS Makarantun Shirya Taro
এছাড়াও পড়ুন:
A binciko mesar da ta ɓace a Kano — Sanusi II
Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya yi kira ga kwamishinan ‘yan sanda Ibrahim Adamu Bakori, da ya tsaurara bincike domin gano mesar da ake zargi mallakin tsohon Akanta-Janar Ahmed Idris ce ta kuɓce kuma ta shiga gari.
Sarkin ya yi jan hankalin ne lokacin da al’ummar unguwar Daneji, bisa jagorancin mai unguwar Malam Abba Lawan suka kai masa koke, kan yadda tsohon Akantan ya ajiye dabbobi masu hadari a gidansa da sunan kiwo, har ake yanka musu shanu domin ciyar da su.
A tsananta hukunci kan masu dukan mata — Sarki Sanusi Yunwa na ƙara tsanani a Arewa maso Gabashin Nijeriya — ICRCSarkin ya kuma ja hankalin tsohon Akantan kan illar ajiye dabbobin a tsakiyar jama’a, tare da yin kira a gare shi da ya gaggauta dauke su, domin gudun abinda ka-je-ka-zo.
Idan za a iya tunawa dai Aminiya ta rawaito yadda ake zargin Akantan da kiwon namun dajin da suka hada da zakuna, da kada, da macizai da kuma mesa, har ma yake yanka musu shanu a bainar jama’a.
A tattaunawarmu da Mai Unguwar, Malam Abba, ya bayyana mana yadda ya jagoranci al’ummar har gaban Sarki, domin neman dauki.
“Lamarin ya faru kafin ranar Juma’a, amma ba mu samu tabbas ba har sai ranar Juma’ar. Na je na same shi da kaina na yi masa magana, na kuma fada masa illar ajiye dabbobi masu hadari a tsakiyar al’umma ya kuma yi min alkawarin zai kwashe.
“Da fari ma da cewa ya yi ba yanzu zai kwashe ba, sai na ce masa sai sun yi girman da za su hadiye wani tukunna? Sai ya ce “za a dauke”.
“Da na ga bai kwashe ba, sai na rubuta rahoto na aika wa Wakilin Kudu, shi kuma ya aika wa Wakilin Hakimi, har zuwa gaban Sarki.
“A yau kuma mun je gaban Sarki mun sanar da shi halin da ake ciki. Kuma an karanta masa takardarmu, ya kuma bayar da umarnin mu je a rubuta wa kwamishinan ‘yan sanda a hukumance, domin su ne suke da hakkin binciken abinda yake gudana.
“Muna sa ran gobe Talata za a kai takardar in sha Allah,” in ji shi.