ECOWAS Da CORET Sun Shirya Taro Domin Cigaban Makarantun Fulani A Kaduna
Published: 1st, June 2025 GMT
Kungiyar Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afrika ECOWAS, tare da haɗin gwiwar Kungiyar Haɗin Kan Masu Kiwon Gargajiya ta Afrika CORET, ta shirya taron horaswa domin ƙarfafa fahimta kan tsarin ciyar da ɗalibai a makarantu, musamman a cikin al’ummomin makiyaya a Jihar Kaduna.
Da yake ƙaddamar da taron a Ladugga, cikin Karamar Hukumar Kachia ta Jihar Kaduna, Ko’odinetan Shirin na CORET, Dr.
Wannan shiri, wanda ke samun goyon bayan haɗin gwiwa daga Swiss Cooperation, na nufin tallafa wa makarantun Fulani da ke Ladugga a Kaduna da kuma Maigatari a Jihar Jigawa, inda ita kuma CORET ke zama jagorar aiwatar da shirin a jihohin biyu.
Ko’odinetan Shirin, Dr. Abdu Umar Ardo ya ce horon yana da nufin ƙarfafa ƙwarewar Kwamitocin Gudanar da Makarantu (SBMC), Ƙungiyoyin Iyaye Mata da na PTA, domin tallafa wa ilimin ‘ya’ya mata da rage yawan yaran da ke zaman gida ba tare da zuwa makaranta ba, musamman a cikin al’ummomin makiyaya.
Dr Ardo wanda ya samu wakilincin Baban Jami’in Sa Ido da Kimantawa na CORET, Alhaji Bimbi Adamu Tahir, ya shawarci mahalarta taron su yi amfani da ilimin da suka samu domin amfanar da al’ummominsu.
A nata jawabin, Shugabar Ƙungiyar Reube Fulbe Development Rights Initiative, Hajiya Halima Yoman, ta jaddada muhimmancin haɗa Ƙungiyoyin Iyaye Mata da Kwamitocin Gudanarwar Makarantu domin kara yawan yaya mata a makarantu.
Ta ce hakan zai taimaka wajen shawo kan matsalar ƙarancin halartar ‘ya’ya mata a makarantun Fulani, tana mai cewa “Ilmantar da mace kamar ilmantar da gaba ɗaya al’umma ne.”
A nata jawabin, Wakiliyar Hukumar Ba da Ilimin Bai Ɗaya ta Jihar Kaduna (SUBEB), Hajiya Hauwa’u Muhammad, ta yi karin bayani game da aikin Kwamitin kula da makarantu kamar haka.
“Kwamitocin Gudanar da Makarantu suna zama hanyar sadarwa tsakanin makaranta da al’umma, inda suke ƙarfafa shiga tsakanin iyaye da shugabannin al’umma da ƙungiyoyi na cikin gida wajen gudanar da harkokin makaranta.”
“Suna kuma marawa baya shigar ‘ya’ya mata da sauran marasa galihu makaranta, ta hanyar warware matsalolin al’ada da na zamantakewa da ke hana su halarta.”
“Kwamitocin na taimakawa wajen sa ido kan ingancin koyarwa da karatun ɗalibai da malamai, domin tabbatar da gaskiya da inganci a harkar ilimi.”
Wasu daga cikin mahalarta taron da suka yi magana da Radio Nigeria Kaduna sun nuna farin cikinsu, inda suka bayyana taron a matsayin mai matuƙar amfani kuma daidai lokacin da ake bukata.
Sun kuma tabbatar wa CORET cewa za su yi amfani da ilimin da suka samu wajen inganta halartar makaranta da gudanar da ita a al’ummominsu.
Taron ya mayar da hankali ne kan manyan al’ummomin Fulani guda uku da ke Ladugga a Kachia: Wuro Nyako da Mbela Biradam da kuma Tiggirde.
COV: Adamu Yusuf
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: ECOWAS Makarantun Shirya Taro
এছাড়াও পড়ুন:
Kotu ta dakatar da babban taron PDP na ƙasa
Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta dakatar da jam’iyyar PDP daga gudanar babban taronta na ƙasa da aka shirya yi a Ibadan, Babban Birnin Jihar Oyo, a watan gobe.
Mai shari’a James Omotosho ne, ya bayar da wannan umarni, yayin da yake yanke hukunci kan wata ƙara da aka shigar domin sanin ko jam’iyyar PDP na da ikon ci gaba da shirya taron da aka tsara gudanarwa a ranakun 15 da 16 ga Nuwamba.
Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4mWaɗanda suka shigar da ƙarar sun haɗa da Austine Nwachukwu, shugaban PDP na Jihar Imo; Amah Abraham Nnanna, shugaban PDP na Jihar Abiya da Turnah George, sakataren PDP na yankin Kudu maso Kudu.
Waɗanda ake ƙarar sun haɗa da Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC), PDP, Sakataren Jam’iyyar na Ƙasa, Samuel Anyanwu, Sakataren shirya taruka na jam’iyyar, Umar Bature, Kwamitin Ayyuka na jam’iyyar na Ƙasa (NWC) da Kwamitin Zartarwa na jam’iyyar na Ƙasa (NEC).
Masu shigar da ƙarar sun kasance ’yan tsahin Nyesom Wike ne.
Sun roƙi kotu da ta hana gudanar da taron, inda suka bayyana cewar jam’iyyar ta saɓa wa dokokinta, Kundin Tsarin Mulkin Najeriya na 1999, da kuma Dokar Zaɓe wajen shirya taron.
Lauyansu ya shaida wa kotu cewa: “Ba a gudanar da taron wakilai a jihohi 14 ba don haka shirin taron ya saɓa wa doka.”
Sai dai PDP ta kare kanta, inda ta ce lamarin na harkokin cikin gidan jam’iyyar ne, don haka bai kamata kotu ta tsoma baki ba.
Jam’iyyar ta zargi masu ƙarar da ƙoƙarin tayar da rikici domin hana ta gudanar da sabon zaɓen shugabanni.
Aminiya ta ruwaito cewa wannan rikici ya ƙara dagula al’amura a jam’iyyar PDP.
Sakataren jam’iyyar na ƙasa, Sanata Samuel Anyanwu, a baya ya yi zargin cewa an yi amfani da hannunsa na bogi a takardun da aka aike wa INEC game da shirya taron.
Amma shugabancin jam’iyyar ya ƙaryata wannan zargi.
A halin yanzu, Kwamitin Shirya Taron na Ƙasa (NCOC) ya ɗage tantance ’yan takara da aka tsara gudanarwa a ranar 28 ga watan Oktoba.
Mutane da dama na ganin ɗage tantance ’yan takarae na da nasaba da jiran sakamakon hukuncin kotu kafin a ci gaba da shirye-shirye.