Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Ta Iran Ya Ce: Taron Kungiyar BRICS Zai Kawo Bunkasar Tattalin Arziki
Published: 1st, June 2025 GMT
Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci ta Iran ya bayyana cewa: Taron kungiyar BRICS wata dama ce ta bunkasa alaka mai karfi ta tattalin arzikin duniya
Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci ta Iran Mohammad Baqir Qalibaf ya bayyana cewa: Halartar tawagar wakilan majalisar dokokin Jamhuriyar Musulunci ta Iran a zauren majalisar dokokin BRICS wata dama ce mai kima ta bunkasa alaka da kasashe masu karfin tattalin arziki na duniya da kuma fuskantar takunkumi.
A wata sanarwa da ya fitar a yammacin jiya Asabar kafin ya tashi zuwa wasu kasashen Latin Amurka uku da kuma halartar taron majalisar dokokin kasashen kungiyar BRICS, Qalibaf ya ce: Za su zagaya kasashen Latin Amurka, inda zasu fara da kasar Venezuela, bisa gayyatar da shugaban majalisar dokokin kasar ya yi masa, domin karfafa alaka a fannonin tattalin arziki, siyasa, da al’adu.
Haka nan kuma yayi nuni da kebantattun kyawawan halayen kasashen Latin Amurka, yana mai bayyana cewa: Wannan yanki mai yawan al’umma sama da miliyan 600, yana da kyakkyawar alaka da Iran a fagen kasa da kasa, kuma dukkaninsu suna yin Allah wadai da daukan matakin bangare guda, kuma suna goyon bayan bangaren hadin kai. Wannan ya ba da dama mai kyau na bunkasa alakarsu da Jamhuriyar Musulunci.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Musulunci ta Iran majalisar dokokin
এছাড়াও পড়ুন:
MDD : Gaza na cikin bala’i mafi muni tun soma yaki a Zirin a Oktoban 2023
Wani rahoto da ofishin kula da ayyukan jin kai na Majalisar Dinkin Duniya ya fitar, ya nuna cewa Gaza na fuskantar bala’i mafi muni tun soma yaki a Zirin a watan Oktoban 2023.
Wakilin Majalisar Dinkin Duniya na musamman kan hakkin bil adama a yankunan Falasdinawa da aka mamaye ya zargi gwamnatin Isra’ila da yin amfani da batun agajin jin kai da gangan domin ci gaba da aiwatar da munanan laifukan da take aikatawa a Gaza.
Francesca Albanese a cikin wata sanarwa da ta fitar ta ce: “Dukkan wadannan matakan an boye su ne a karkashin sunan agaji don karkatar da hankulan kasashen duniya.”
A wani labarin kuma Kakakin Majalisar Dinkin Duniya Stéphane Dujarric ya shaida wa manema labarai a ranar Juma’a da ta gabata cewa: Bukatun jin kai a Gaza ya karu sosai bayan kusan kwanaki 80 na hana shigar da tallafi a zirin.
‘’tallafin da ake samu a yanzu haka bai wadatar ba wajen biyan bukatun mutane sama da miliyan 2.1 da ke bukatar agajin gaggawa. » inji shi.
Adadin wadanda sukayi shahada a wannan yanki na Falasdinu tun daga ranar 7 ga watan Oktoban shekarar 2023 ya kai mutane 54,381, a cewar ma’aikatar lafiya ta Gaza.