Aminiya:
2025-07-06@19:06:43 GMT

Tottenham ta lashe Gasar Europa bayan doke Manchester United

Published: 22nd, May 2025 GMT

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Tottenham Hotspur ta zama zakarar Gasar Europa bayan doke Manchester United da ci ɗaya mai ban haushi.

Tottenham ta kafa tarihi a yau Laraba na lashe kofi tun bayan shekara 17 da ta lashe wani babban kofi.

Zargin Satar Fasaha: Kotu ta sanya ranar yanke hukunci kan shari’ar BBC Sojoji da ’yan siyasa na taimaka wa Boko Haram da bayanai — Zulum

Ƙungiyar ta samu nasara ne ta hannun ɗan wasan gabanta, Johnson a minti na 42 kafin tafiya hutun rabin lokaci.

Ƙungiyoyin biyu sun kara da juna ne a daren ranar Laraba a filin wasa na San Mamés da ke ƙasar Sifaniya.

Hakan na nufin Manchester United ta ƙare kakar wasa ta bana ba tare da ta lashe kofi ko ɗaya.

A yanzu haka Manchester United na matsayi na 16 a gasar Firimiyar Ingila, yayin da Tottenham Hotspur ke biye mata a matsayi na 17.

Gasar Firimiyar Ingila ya rage wasa ɗaya kacal a kammala, wanda tuni Liverpool ta lashe gasar makonni biyu da suka gabata.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Firimiyar Ingila Gasar Europa Kwallon Kafa matsayi Zakara Kofi

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning, ta bayyana a gun taron manema labarai da aka yi a yau Juma’a cewa, Sin na fatan kara hadin gwiwa da Ghana, don gaggauta bunkasuwar huldarsu ta abota bisa manyan tsare-tsare.

Yayin da Mao Ning take tsokaci game da cika shekaru 65 da kulla huldar diplomasiyya tsakaninsu, ta ce a ranar 5 ga watan nan da muke ciki, za a cika shekaru 65 da kalluwar huldar tsakanin kasashen biyu. Ta ce, Ghana na daya daga cikin kasashen Afirka dake kudu da hamadar Sahara da suka riga sauran kasashe kulla huldar diplomasiyya da jamhuriyar jama’ar Sin, kuma ita ce kasa ta farko a wannan yanki da tsoffin shugabannin Sin suka ziyarta. Ta ce a shekarar bara, bangarorin biyu sun tabbatar da kafa huldar abota bisa manyan tsare-tsare a tsakaninsu, kuma Sin tana fatan kara hadin gwiwa da Ghana don amfani da wannan zarafi mai kyau wajen zurfafa dankon zumunci dake tsakaninsu, ta yadda al’ummun kasashen biyu za su ci gajiya. (Amina Xu)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson
  • Kofin Duniya: Real Madrid Za Ta Fara Da PSG A Semi Final
  • An kama ɗan Najeriya yana taimaka wa Rasha a yaƙinta da Ukraine
  • Bayern Munich Ta Fara Zawarcin Marcus Rashford
  • Ana Tuhumar Tsohon Ɗan Wasan Arsenal Thomas Partey Da Laifin Fyaɗe A Ƙasar Ingila
  • Hadiman gwamnan Kano sun haura 300 bayan naɗa wasu sabbi 19
  • Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu
  • ’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja
  • Haɗarin Da Ke Ƙunshe Da Jin Ɓangare Ɗaya Na Labari
  • Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC