Aminiya:
2025-05-22@01:50:08 GMT

Tottenham ta lashe Gasar Europa bayan doke Manchester United

Published: 22nd, May 2025 GMT

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Tottenham Hotspur ta zama zakarar Gasar Europa bayan doke Manchester United da ci ɗaya mai ban haushi.

Tottenham ta kafa tarihi a yau Laraba na lashe kofi tun bayan shekara 17 da ta lashe wani babban kofi.

Zargin Satar Fasaha: Kotu ta sanya ranar yanke hukunci kan shari’ar BBC Sojoji da ’yan siyasa na taimaka wa Boko Haram da bayanai — Zulum

Ƙungiyar ta samu nasara ne ta hannun ɗan wasan gabanta, Johnson a minti na 42 kafin tafiya hutun rabin lokaci.

Ƙungiyoyin biyu sun kara da juna ne a daren ranar Laraba a filin wasa na San Mamés da ke ƙasar Sifaniya.

Hakan na nufin Manchester United ta ƙare kakar wasa ta bana ba tare da ta lashe kofi ko ɗaya.

A yanzu haka Manchester United na matsayi na 16 a gasar Firimiyar Ingila, yayin da Tottenham Hotspur ke biye mata a matsayi na 17.

Gasar Firimiyar Ingila ya rage wasa ɗaya kacal a kammala, wanda tuni Liverpool ta lashe gasar makonni biyu da suka gabata.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Firimiyar Ingila Gasar Europa Kwallon Kafa matsayi Zakara Kofi

এছাড়াও পড়ুন:

Sharhin Bayan Labarai: Dandalin Tattaunawa Na Tehran

Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka, sharhin bayan labarummu zai yi magana dangane da taron tattaunawa ta Tehran wanda aka bude a ranar Lahadi 18 ga watan mayu a nan Tehran.

A ranar Lahadi 18 ga watan Mayu da muke ciki ne aka bude taron tattaunawa da ta Tehran ta farko a nan Iran, don tattauna batutuwan da suka shafi kasashen yankin yammacin Asiya. Inda shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkiyan da kuma ministan harkokin wajen kasar Iran suka gabatar da jawaban farko a taron.

An sami halattan baki daga kasashe 53 daga cikinsu akwai jami’an gwamnatoci wadanda suka hada da ministoci  masana da shuwagabannin cibiyoyin bincike da bada shawarori na kasashen duniya da dama.

Daga cikin bakin akwai ministan harkokin wajen kasar Oman Badr bin Hamad Al Busaidi wanda ya fadawa tashar talabijin ta Presstv kan cewa yankin yammacin Asiya a halin yanzu yana fuskantar matsaloli wadanda suke bukatar a tattaunasu tsakanin kasashen yankin. Ya kuma kara da cewa kasar Omman a shirye take ta shiga tattaunawa don fahintar juna ko da da wanda take da sabani sosai da ita ne kuwa. Ministan ya bada misali da rikicin kasar Falasdinu, wanda ya zarce dukka matsaloli yankin yammacin Asiya, har ya zama matsala ta kasashen duniya.

Ya ce: Abinda Falasdinawa suke fuskanta a hannun HKI a halin yanzu ya zama babban matsala da damuwa ga kasashen duniya da dama.

Albusaiti ya bayyana cewa abinda yake faruwa a kasar Falasdinu, bai kamata ya auku ba, ko kuma ba zai faru ba, da anbi hanyar tattaunawa tun lokaci bai kure ba. Ya kammala da cewa “Tattaunawar Tehran” wata dama ce ga wadanda suka yi Imani da tattaunawa a matsayin hanya tilo ta warware matsaloli tsakanin kasashe.

Sai kuma ministan harkokin wajen kasar Tajakisatn wanda ya bayyana cewa kasashen duniya suna bukatar tattaunawa mai zurfi don warware matsaloli masu yawa da take fama da su.

Sirajuddin Muhriddin ya kara da cewa kasashen duniya suna bukatar tattaunawa mai zurfi da kuma gudanar da bincike masu yawa don warware dimbin matsalolin da ake fuskanta da suka shafi tsaro da tabbatar da zaman lafiya a duniya.

Ministan ya bayyana a cikin jawabinda ya gabatar kan cewa lalle kasashen duniya suna bukatar tattaunawa saboda ganin yadda al-amura suke sauyawa a cikinta da sauri.

Yace wuce gona da iri da tsatsauran ra’ayi wadanda suka kaiwa ga tashe-tashen hankula sun zama babban barazana ga dukkan mutanen a duniya. Ya yi kira ga kasashen duniya su gaggauta daukan bai-daya don magance da kuma kawo karshen kara fadadar wadannan matsaloli.

Ya bukaci a samar da shirin bai daya na samar da tsaro a wannan yankin don tabbatar da tsaro da zaman lafiya a cikinsa.

Ministan harkokin wajen kasar Tajakistan ya kammala da cewa, wasu tsare-tsaren da ake da su a halin yanzu a yankin ba zasu iya tabbatar da zaman lafiya da kuma warware matsaloli tsakanin kasashen yankin ba, don haka akwia bukatar tattaunawa mai zurfi a tsakaninsu don cimma wannan manufar.

Sai kuma sakataren majalisar tsaro ta kasar Armenia wanda ya bayyana cewa kasarsa tana kokarin tabbatar da tsawo da zaman lafiya a kasar, da kuma makobta.

Armen Grigoryan ya bayyana cewa shirin gwamnatin kasar na (Drossroad For Peace) wanda aka kaddamar da shi a cikin watan Octoban shekara ta 2023 yana dauke da manufar bude hanyoyin bunkasa tattalin arzikin yankin wanda ya dade yana tseye baya motsawa, ya zama ya samar da cudayya da juna a yankin saboda ci gaban kowa. Ya ce munyi Imani kan cewa wannan shirin yana da muhimmanci wajen bunkasa tattalin arziki wanda kuma zai kai ga samar da zaman lafiya mai dorewa a yankin.

Sannan tsohon firai ministan kasar Iraqi Adil Abdulmahdi, a jawabinda ya gabatar a dandalin tattaunawa na Tehran wato “Tehran Dialoque Furum”,  ya ce kasashen larabawa da sauran kasashen duniya duk, sun kasa warware rikicin Falasdinawa da HKI. Ya kuma kara da cewa kissan kiyashin da ke faruwa a Gaza, wata babbar matsala ce wacce ta girgiza dukkan mai lamiri a cikin zuciyarsa.

Abdul Mahdi ya cewa hatta kotun kasa da kasa ta ICC ta kasa dakatar da kisan kiyashin da HKI take aikawa a Gaza wanda ya nuna irin lalacewra da al-amura suka yi a duniya a yau.

Tsohon firai ministan ya kara da cewa abinda yake faruwa a Gaza, Holocus ne a fili wanda al-amarin bai tsaya nan ba, birane a yankin yamma da kogin Jordan da Lebanon duk suna fauskantar wannan matsalar daga HKI.

Daga karse yayi kira ga kasashen duniya su tashi su nuna cewa sun damu da binda ke faruwa a Gaza, mai yuwa mu kawo karshen wannan kissan kare dangin.

Abdul Mahdi ya rufe da cewa tarihi zata riki wasu da dama da shirun da suka yi a ta’asar da HKI take aikawata a Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kocin Super Eagle Ya Gayyaci Ahmed Musa Buga Gasar Kofin Unity A Landan
  • Tottenham Ta Doke Manchester United A Wasan Karshe Na Europa 
  • Bayan Shekaru 42 Babu Kofi, Tottenham Ta Lashe Gasar Europa League Akan Manchester United 
  • Bayan Shekaru 42, Tottenham Ta Lashe Gasar Europa League Akan Manchester United 
  • Hajjin 2025: Kashi 79 na maniyyatan Najeriya sun isa Saudiyya – NAHCON
  • Gasar Wasanni Ta Kasa: FCT Ta Lallasa Borno Da Ci 4-1 A Wasan Farko
  • Sharhin Bayan Labarai: Dandalin Tattaunawa Na Tehran
  • Everton Ta Yi Ban Kwana Da Goodison Park
  • CAN U20 : Afirka ta Kudu ta lashe kofi na farko