Kotu Ta Soke Umarnin Kwace Filin Asibitin Tiamin, Ta Umarci Gwamnatin Kano Ta Biya Diyyar Biliyan ₦2.6bn
Published: 22nd, May 2025 GMT
A wani hukunci da ya yanke a ranar Laraba, alkalin kotun, Ibrahim Karaye, ya ce soke hakkin wanda ya shigar da kara ya sabawa ka’ida, ya sabawa kundin tsarin mulkin kasa, kuma hukuncin ba shi da tushe balle makama.
Karaye ya ci gaba da cewa, sanarwar kwace shaidar mallakar filin a cikin wata wasika mai dauke da kwanan watan Satumba 3, 2021, daga ofishin kula da filaye na jihar Kano, an yi ta ne ba tare da an yi shari’a ta adalci ba, wanda hakan ya saba wa tanadin dokar amfani da filaye.
Alkalin ya ci gaba da bayyana cewa, takardar shaidar mallakar fili ta asali mai lamba LKN/COM/2017/116 [wacce aka sake shedawa a matsayin LPKN 1188], MLKN01622, da MLKN01837 – suna nan da inganci kuma sahihai.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Na’im Kassim: Kare Kasa Ba Ya Da Bukatuwa Da Izinin Kowa
Babban magatakardar kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon Sheikh Na’im Kassim ya mayar da martani ga wadanda suke son, kungiyar ta mika makamanta, yana mai cewa; Ku fara da neman makiya su fice daga cikin Lebanon, domin babu hankali ace ba ku cewa komai akan ‘yan mamaya,ya zamana kuna neman wanda yake gwgawarmaya ya ajiye makamansa.”
Sheikh Na’im Kassim ya kuma ce: Duk wanda ya amince da mika wuya, ya yi, amma mu ba za mu laminta da hakan ba. Mu almajiran makarantar Imam Hussain ( a.s) ne da yake cewa: Ba Za Mu Taba Lamunta Da Kaskanci Ba.”
Sheikh Na’im Kassam ya ce: Wadanda suke jingina da kasashen waje, suna kuskuren lissafi, domin masu gwgawarmaya ba su ganin wani kwarjinin abokan gaba, ba kuma za su sarayar da hakkokinsu ba.”
Babban magatakardar kungiyar ta Hizbullah ya kuma kara da cewa: Babban ci gaba na hakika da aka samu shi ne ‘yanto da kasa, muna kuma cikin Shirin ci gaba da yin haka a kodayaushe.”
Sheikh Na’im Kassim ya jaddada cewa;raya lokacin shahadar Imam Hussain ( a.s), raya musulunci ne da dukkanin bangarorinsa, da kuma manhajarsa.
Haka nan kuma ya ce; Musulunci wanda Imam Hussian ( a,s) da iyalan gidansa su ka kare shi, shi ne fidirar mutum tabbatacciya, yana kuna ayyana nauyin da ya rataya akan kowance mutum daidai da gwargwadon dabi’arsa ta namiji ko mace. Nauyin da ya rataya a wuyan namiji shi ne daukar makami domin yin yaki na bayar da kariya, ita kuwa mace ba a dora mata yin hakan ba,amma a lokaci daya abokiyar tarayya ce a cikin jihadi ta hanyar rawar da take takawa a bayan fagen daga, da su ka hada yin tarbiyya da ayyukan da muhimmancinsu bai gaza na namiji a fagen daga ba.