Kotu Ta Soke Umarnin Kwace Filin Asibitin Tiamin, Ta Umarci Gwamnatin Kano Ta Biya Diyyar Biliyan ₦2.6bn
Published: 22nd, May 2025 GMT
A wani hukunci da ya yanke a ranar Laraba, alkalin kotun, Ibrahim Karaye, ya ce soke hakkin wanda ya shigar da kara ya sabawa ka’ida, ya sabawa kundin tsarin mulkin kasa, kuma hukuncin ba shi da tushe balle makama.
Karaye ya ci gaba da cewa, sanarwar kwace shaidar mallakar filin a cikin wata wasika mai dauke da kwanan watan Satumba 3, 2021, daga ofishin kula da filaye na jihar Kano, an yi ta ne ba tare da an yi shari’a ta adalci ba, wanda hakan ya saba wa tanadin dokar amfani da filaye.
Alkalin ya ci gaba da bayyana cewa, takardar shaidar mallakar fili ta asali mai lamba LKN/COM/2017/116 [wacce aka sake shedawa a matsayin LPKN 1188], MLKN01622, da MLKN01837 – suna nan da inganci kuma sahihai.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Nuna Wasu Manyan Fina-Finai 22
Gwamnatin jihar Kano ta dakatar da nuna wasu manyan fina-finai masu dogon zango 22 sakamakon zarginsu da saɓa ƙa’idar hukumar.
Cikin wata sanarwa da jami’in hul da jama’a na hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman ya fitar ya ce shugaban hukumar Abba Al-Mustapha ne bayar da umarcin saboda a cewarsa masu shirya fina-finan sun saɓa ƙa’idojin hukumar waɗanda suka tanadi cewa dole ne hukumar ta tace su kafin fitar da su.
Wasu daga cikin fina-finan da dakatarwa ta shafa sun haɗa da
Dadin Kowa
Labarina
Gidan Sarauta
Manyan Mata
Dakin Amarya
Kishiyata
Garwashi
Jamilun Jiddan
Mashahuri
Wasiyya
Tawakkaltu
Mijina
Wani Zamani
Mallaka
Kudin Ruwa
Boka Ko Malam
Wayasan Gobe
Rana Dubu
Fatake
Shahadar Nabila
Tabarmar
Rigar Aro
An umurci masu shirya fina-finan da abin ya shafa da su dakatar da duk wani nau’i na watsa shirye-shirye ko yawo nan da nan tare da gabatar da abubuwan da ke cikin su don amincewar tantancewa a cikin mako guda daga Litinin, Mayu 19 zuwa Litinin, Mayu 26, 2025.
Hukumar ta kuma yi kira ga gidajen Talabijin da Hukumar Yada Labarai ta Najeriya (NBC) da su taimaka wajen tabbatar da wadannan ka’idoji, tare da yin daidai da kokarin inganta kwarewa da bunkasar masana’antar Kannywood.
KHADIJAH ALIYU