Sojojin Sudan sun karbe iko da sansanin dakarun kai daukin gaggawa na karshe a birnin Khartoum fadar mulkin kasar

Sojojin Sudan sun ci gaba da dama a jihohin Kordofan da Darfur, inda suka bar birnin Nahud da ke yammacin Kordofan, wanda sojojin suka killace birnin ta kowane bangare.

Sojojin Sudan sun samu nasarar karbe ikon yankin Atrun mai mahimmanci a Arewacin Darfur, tare da bude hanyar shiga sauran garuruwan Darfur gaba daya.

Bayan kazamin fada tsakanin sojojin Sudan da dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces a yankin Al-Saliha da ke kudancin Omdurman, wanda ya dauki tsawon sama da wata guda ana gwabzawa, sojojin sun samu nasarar mamaye yankin gaba daya, sai dai wasu kananan yankuna da sojojin ke hadawa, a cewar kakakin rundunar sojin Sudan.

Rundunar kungiyar Rapid Support Forces ta dakaraun kai daukin gaggawa ta mayar da martani ta hanyar kai hari a wani ma’ajiyar makamai a tsakiyar Omdurman tare da wani jirgin sama maras matuki.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Harkokin Wajen Iran Da Tawagarsa Sun Isa Kasar Brazil Don Halartar Taron BRICS Karo Na 17

Ministan harkokin wajen kasar Iran ya tafi kasar Brazil don halartar taron BRICS karo na 17

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Ismail Baqa’i ya sanar da isar ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi a birnin Rio de Janeiro domin halartar taron kasashe mambobi a kungiyar BRICS karo na 17.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Ismail Baqa’i ya bayyana a cikin wata sanarwa cewa: Tawagar kasar Iran karkashin jagorancin ministan harkokin wajen kasar Abbas Araqchi za ta halarci taron kasashen BRICS.

Baqa’i ya rubuta a shafinsa na sada zumunta cewa: “Sun isa birnin Rio de Janeiro na Brazil, domin halartar taron kasashen BRICS karo na 17.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Harkokin Wajen Iran Da Tawagarsa Sun Isa Kasar Brazil Don Halartar Taron BRICS Karo Na 17
  • Tsoro, Fargaba Da Wahala: ‘Bala’in Da Muka Gani A Yakin Sudan
  • Sojojin HKI Kimani 40 Ne Suka Halaka Ko Suka Jikata A Jiya Jumma’a A Yankin Shuja’iyya Na Birnin Gaza
  • Shugaban Kasar Iran Ya Gabatar Da Jawabio A Taron Kolin Kungiyar ECO Musamman Kan Harin Da Kasarsa Ta Fuskanta
  • Ayatullahi Khatami Ya Ce Hukuncin Da Ya Cancanci Trump Da Netanyahu Shi Ne Kisa Saboda Zubar Da Jinin Bil’Adama
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kashe Masu Neman Karbar Kayan Agaji A Gaza
  •  A Yau Juma’a Ne Ake Gudanar Da Taron Karrama Shahid Birgediya Janar Husain Salami A Nan Birnin Tehran
  • Kwamandan Sojojin Iran Ya Ziyarci Gidan Babban Jami’in Sojin Kasar Da Ya Yii Shahada Lokacin Yakin Baya-Bayan Nan
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Sake Aiwatar Da Kisan Kare Dangi Kan ‘Yan Gudun Hijiran Falasdinawa
  • Buhari ba ya cikin mawuyacin hali — Bashir Ahmad