Aminiya:
2025-07-06@14:17:40 GMT

Hukumar tace fina-finai ta soke lasisin gidajen gala 8 a Kano

Published: 21st, May 2025 GMT

Hukumar Tace Fina-finai da Ɗab’i ta Jihar Kano, ta soke lasisin gidajen wasannin gala guda takwas bisa karya wasu dokokinta.

Idan za a tuna a kwanakin baya hukumar, ta soke lasisin wasu gidajen galar bisa samun su da laifin karya dokar hukumar.

Ma’aikatan wutar lantarki sun tsunduma yajin aiki a Kano Sojoji da ’yan siyasa na taimaka wa Boko Haram da bayanai — Zulum

Cikin sanarwar da kakakin hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman, ya fitar, ya zayyano wuraren da hakan ta shafa da suka haɗa da Hamdala Entertainment, Lady J Entertainment, Ɗan Hausa Entertainment da Ni’ima.

Sauran sun haɗa da Babangida Entertainment, Harsashi Entertainment, da kuma Wazobiya.

Idan ba a manta ba hukumar a baya-bayan nan ta dakatar da haska wasu fina-finai 22 da suka haɗa da Dadin Kowa, Labarina, Garwashi, Gidan Sarauta da wasu.

Amma bayan wani taron masu ruwa da tsaki na Kannywood an bai wa masu shirya fina-finan wa’adin mako guda don tantance su.

A ranar Talata ma hukumar ta dakatar da yin tallan magungunan gargajiya a cikin fina-finai ko a kan titin har sai an tantance su.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hukumar Tace Fina finai da Dab I ta Kano

এছাড়াও পড়ুন:

Ambaliya da iska sun rushe gidaje 171 a watanni biyu a Gombe – SEMA

Hukumar Bayar da agajin gaggawa ta Jihar Gombe (SEMA) ta bayyana cewa, ambaliya da iska mai ƙarfi sun rushe da lalata gidaje 171 a yankunan jihar cikin watanni biyu da suka gabata, lamarin da ya haddasa asara da kuma mutuwar yara huɗu.

Sakataren zartarwa na Hukumar SEMA, Malam Abdullahi Haruna Abdullahi ne ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Gombe, inda ya ce iftila’in ya shafi ƙananan hukumomin Dukku da Kwami da Gombe da Akko.

Harin Filato: Remi Tinubu ta ba da gudummawar Naira biliya 1 Buhari ba ya cikin mawuyacin hali — Bashir Ahmad

“Mun samu rahoton rushewar gidaje 87 a Dukku, 27 a Kwami, 30 a Gombe da kuma 27 a Akko, ciki har da wata coci da ambaliya ta lalata.

Haka kuma yara huɗu sun rasa rayukansu, mafi yawansu yara ne,” in ji shi.

Ya bayyana cewa, rashin tsaftar muhalli da kuma yawan sare bishiyoyi na daga cikin abubuwan da suka taimaka wajen haddasa ibtila’in.

Ya yi kira ga al’umma da su daina zubar da shara a cikin magudanan ruwa, tare da amfani da wuraren zubar da shara da gwamnatin jihar ta gina.

“Akwai buƙatar kowa ya taka rawar gani wajen kare muhallinsa, musamman a lokacin damina.

Iyaye su kula da ‘ya’yansu, musamman ma yara ƙanana domin gudun afkuwar hatsarin faruwar hakan,” in ji Malam Abdullahi.

Sakataren SEMA ya kuma yi tir da yawan sare bishiyoyi domin yin gawayi na girki, yana mai cewa hakan yana ƙara haddasa fari da kuma rushewar muhalli.

Sai ya shawarci jama’a su ci gajiyar daminar da ake ciki wajen dasa bishiyoyi a gidajensu da unguwanninsu domin rage ƙarfi da haɗarin iska da kuma yaƙi da hamada.

Malam Abdullahi ya ƙara da cewa, Hukumar SEMA na shirin kai kayan tallafi ga waɗanda ibtila’in ya shafa a sassan jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Jihar Jigawa Ta Bukaci Karamar Hukumar Roni Ta Samar Da Karin Ajujuwa Ga Fulani Makiyaya
  • Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
  • Mutanen unguwa sun kama masu ƙwacen waya a Kano
  • Ma’aikatan MDD Masu Kula Da Ayyukan Makamashin Nukliya Na Kasar Iran Su Fice daga Kasar
  • Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin
  • Hadiman gwamnan Kano sun haura 300 bayan naɗa wasu sabbi 19
  • Abba ya naɗa Ahmed Musa a matsayin Babban Manajan Kano Pillars
  • Majalisar Jigawa Ta Isa Roni A Ci Gaba Da Rangadin Kananan Hukumomi
  • Ambaliya da iska sun rushe gidaje 171 a watanni biyu a Gombe – SEMA
  • Tsohon golan Super Eagles, Peter Rufai ya mutu