HausaTv:
2025-06-16@06:53:41 GMT

Wasu Yahudawa Sun Hana Kayakin Agaji Shiga Yankin Gaza

Published: 21st, May 2025 GMT

Bayan watannin kimani biyu da rabi wanda gwamnatin HKI suka hana kayakin abinci da magunguna shiga yankin zirin Gaza, a jiya talata, gwamnatin Natanyahu ta bada damar a shigo da wasu kadan da kayakin agajin, saboda takurawar wasu shuwagabnni a kasashen yamma.

Amma duk da haka a yau wasu yahudawa fararen hula sun hana wucewar wata mota makare da abinci shigowa zirin gaza daga kofar shiga yankin ta Karen Abu Salem.

Hotunan bidiyo sun nuna yadda jerin gwanon motoci dauke da kayakin agaji zuwa gaza amma wasu yahudawa dauke da tutocin HKI sun zo sun tsaya a gaban daya daga cikinsu suna fadar cewa basu yarda a shigar da kayakin agaji zuwa gaza ba har sai sun mutu gaba daya.

 Sannan a dayan bangaren kuma sojojin HKI rike da bindigogi sun zuba masu ido suna kallo.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

HOTUNA: Yadda aka yi sulhu da ƙasurgumin ɗan fashin daji Ado Aliero a Katsina

Wasu mazauna Jihar Katsina sun yi zaman sulhu da wasu shugabannin ’yan daban daji da suka addabe su.

Wakilinmu ya ruwaito cewa an yi taron sasanci da ’yan bindigar daji ne a Ƙaramar Hukumar Danmusa, wanda rundunar sojoji ke shiryawa, inda Adamu Aliero ya jagoranci sashen ’yan bindigar.

BBC ya ruwaito Kwamishinan Tsaro da Harkokin Ciki Gida na Katsina na cewa al’ummar garin Bicci da ke yankin Ƙaramar Hukumar Danmusa sun zauna tare da Ado Aliero da sauran wasu shugabannin ’yan bindigar aƙalla goma.

“An zauna da Ado Aliero da Kamilu Buzaru da Dogo Nahali da Wada Jargaba da Dahiru Buzu haka ma da Nagoggo,” in ji shi.

Hotuna daga Ahmed Kabiru S/Kuka

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran ta kai sabbin hare-hare birnin Tel Aviv da Haifa
  • HOTUNA: Yadda aka yi sulhu da ƙasurgumin ɗan fashin daji Ado Aliero a Katsina
  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
  • HKI Ta Rufe Filin Saukar Jiragen Sama Na Ben Gorion Tare Da Dauke Jiragenta  Zuwa Waje
  • Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai
  • Iran, ta yi wa Isra’ila ruwan makamai masu linzami
  • Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin
  • Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu