Majalisar Wakilai za ta gabatar da kudurori guda biyar da za su magance manyan kalubale da ke hana ingantaccen aiki a harkar man fetur ta kasa.

Shugaban kwamitin Majalisar kan Albarkatun Man Fetur, Alhaji Alhassan Ado Doguwa, ne ya bayyana hakan yayin wani taro na hadin gwiwa da kwamitin musamman kan matsalar satar danyen mai a Abuja.

Alhaji Alhassan Ado Doguwa ya ce kudurorin da ake shirin gabatarwa, za a gabatar da su ne tare da shugabannin kwamitocin biyu, kuma wani bangare ne na matakan dokoki don tallafawa kokarin gwamnati wajen kare kadarorin man fetur da gas da kuma dakile matsalar satar danyen mai.

Ya bayyana cewa daya daga cikin kudurorin na neman kafa Hukumar Kasa da za ta sami ikon dakile ayyukan  masu lalata bututun mai da gurfanar da su , da kuma aikata wasu laifuka da suka shafi bangaren man fetur.

“Kwamitocin da duk Majalisar baki daya na matukar damuwa da karuwar rashin tsaro da ayyukan laifi a yankunan da ake hakar mai. Wannan mataki na majalisa wata hanya ce ta tallafa wa kokarin gwamnati wajen kare wadannan muhimman kadarorin kasa,” in ji Alhaji Ado Doguwa.

Har ila yau, Alhaji Ado Doguwa ya bayyana cewa daya daga cikin kudurorin da ke karkashin Kwamitin Albarkatun Man Fetur (Sashen Sama), wanda Kakakin Majalisar, Dr Abbas Tajuddeen, ke jagoranta, na neman kafa Hukumar da za ta kula da cire kayan aikin hakar mai da suka tsufa, matsala da ke da matukar muhimmanci ga al’ummomin da ke karbar bakuncin ayyukan man fetur da sauran masu ruwa da tsaki.

 

Salihu Tsibiri 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Dalilin da babu abin da gwamnatin NNPP ta taɓuka a Kano — APC

Ƙungiya mai rajin kishin APC a Kano mai suna APC Patriotic Volunteers, ta ce shekaru biyun da jam’iyyar NNPP ta shafe tana mulkin jihar nakasu ne da ke nuna tsantsar rashin ƙwarewarta a gwamnatance.

A taron da ta gudanar da manema labarai a Kano, ƙungiyar bisa jagorancin shugabanta Alhaji Usman Alhaji (Wazirin Gaya) ta ce nazarin da ta yi wa salon mulkin gwamnan jihar Abba Kabir Yusuf, ya tabbatar mata da gazawarsa wajen haɓaka ɓangarori masu muhimmanci duk da makudan kudaden shiga da gwamnatin tarayya ke bata, da kuma kudaden shiga na cikin gida da take samu.

Mokwa: Zulum ya kai ziyarar jaje Neja, ya bayar da tallafin N300m Ana zargin uwa da kashe ’yarta kan Naira 100 a Zariya

“Babu ayyukan a zo a gani idan ka duba biliyoyin da ke shiga jihar.”

Kazalika kungiyar ta zargi gwamnan da wawure Naira biliyan 1.6 da aka ware domin sayen mai da sauran kayan aiki na tsawon watanni uku a ma’aikatar ruwa ta Kano, baya ga gazawa wajen biyan ma’aikata sabon mafi ƙarancin albashi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Farashin fetur ya tashi a kasuwar duniya bayan harin Isra’ila a Iran
  • Gwamnatin Tarayya Ta Himmatu Wajen Inganta Karfin Sashen Fetur Da Gas Na Cikin Gida
  • Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka
  • An Kaddamar Da Bikin Gabatar Da Jerin Shirye-shiryen Telebijin Da Fina-finai Na CMG A Birnin Astana
  • Hajjin 2025: Yadda Alhazan Nijeriya 7 Suka Rasa Rayukansu A Saudi Arabiya
  • Yadda Badakalar Tallafin Man Fetur Ta Zame Wa Nijeriya Alakakai
  • Ministan man Fetur na Kasar Iran Yace Amurka Ta Kasa Hana Iran Saida Danyen Man Fetur Na Kasar
  • Dalilin da babu abin da gwamnatin NNPP ta taɓuka a Kano — APC
  • Jagora Ya Bambance Tsakanin Majalisun Dokokin Kasashe A Fagen Gudanar Da Ayyukan Kasa
  • He Lifeng Ya Bukaci Amurka Da Ta Warware Takaddamar Cinikayya Da Sin Ta Hanyar Tattaunawa Da Hadin Gwiwa