Majalisar Wakilai Za Ta Gabatar Da Dokoki Biyar Don Gyara Bangaren Man Fetur
Published: 21st, May 2025 GMT
Majalisar Wakilai za ta gabatar da kudurori guda biyar da za su magance manyan kalubale da ke hana ingantaccen aiki a harkar man fetur ta kasa.
Shugaban kwamitin Majalisar kan Albarkatun Man Fetur, Alhaji Alhassan Ado Doguwa, ne ya bayyana hakan yayin wani taro na hadin gwiwa da kwamitin musamman kan matsalar satar danyen mai a Abuja.
Alhaji Alhassan Ado Doguwa ya ce kudurorin da ake shirin gabatarwa, za a gabatar da su ne tare da shugabannin kwamitocin biyu, kuma wani bangare ne na matakan dokoki don tallafawa kokarin gwamnati wajen kare kadarorin man fetur da gas da kuma dakile matsalar satar danyen mai.
Ya bayyana cewa daya daga cikin kudurorin na neman kafa Hukumar Kasa da za ta sami ikon dakile ayyukan masu lalata bututun mai da gurfanar da su , da kuma aikata wasu laifuka da suka shafi bangaren man fetur.
“Kwamitocin da duk Majalisar baki daya na matukar damuwa da karuwar rashin tsaro da ayyukan laifi a yankunan da ake hakar mai. Wannan mataki na majalisa wata hanya ce ta tallafa wa kokarin gwamnati wajen kare wadannan muhimman kadarorin kasa,” in ji Alhaji Ado Doguwa.
Har ila yau, Alhaji Ado Doguwa ya bayyana cewa daya daga cikin kudurorin da ke karkashin Kwamitin Albarkatun Man Fetur (Sashen Sama), wanda Kakakin Majalisar, Dr Abbas Tajuddeen, ke jagoranta, na neman kafa Hukumar da za ta kula da cire kayan aikin hakar mai da suka tsufa, matsala da ke da matukar muhimmanci ga al’ummomin da ke karbar bakuncin ayyukan man fetur da sauran masu ruwa da tsaki.
Salihu Tsibiri
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato
Mataimakinsa kan harkokin majalisa Honarabul Attahiru Danmadi ne ya wakilci dan majalisar ya kuma tabbatarwa wadanda lamarin ya shafa kokarinsa kan daukar matakan da suka kamata domin tabbatar da tsaron rayukan su da dawowa da zaman lafiya a yankunan.
Garuruwan da ‘yan bindigar suka tarwatsa a gundumar Kuchi sun hada da Fakku, sha’alwashi, tulluwa da Rafin- gora a inda mutane bakwai suka rasa rai. A gundumar Jabo kuwa kauyukan da lamarin ya shafa su ne; Gesolodi, Hilya, Guraye, Guma, Chakai, Modo, Badariya, Tafki, Balera, Gudumawa da Rafin shinka.
“Mun girgiza kwarai da wannan halin da kuke ciki. A matsayina na wakilin ku, zan ci-gaba da kokarin da ya kamata a majalisa domin ganin jami’an tsaro sun kawo karshen wannan ta’addancin.”
Dan Majalisar ya ce ya gabatar da bukata ga Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Kasa domin tallafawa wadanda lamarin ya shafa kuma zai ci- gaba da bibiya domin ganin tallafin ya samu cikin lokaci.
Ya ce yana kokarin ganin rundunar sojoji ta kara tura wadatattun jami’ai tare da tallafa masu domin yakar ‘yan ta’addan da wanzar da zaman lafiya a yankunan.
Tallafin kayan abinci na gaggawa da dan majalisar ya bayar sun hada da buhuhuwan masara, gero, garin kwaki da kuma kuli- kuli.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp