A yau Talata ne dai sojojin Sudan su ka sanar da cewa, baki dayan jihar Khartum ta zama ‘yantacciya daga dakarun kai daukin gaggawa na                 ( RSF), bayan da  su ka kwace iko da fadar shugaban kasa dake cikin birnin a watan Maris.

Kakakin rundunar sojan Sudan ya sanar da cewa; Sojojin kasar da dukkanin bangarorinsu, suna ci gaba da sauke nauyin da yake kansu na fada da rundunar kai daukin gaggawa da masu taimaka mata a cikin yanki da kuma a fagen kasa da kasa.

Kakakin rundunar sojan kasar ta Sudan ya kuma ce; Sojojin na kasar Sudan suna samun nasarori a kowace rana.

Wata majiyar soja ta sanar da tashar talabijin din aljazira cewa; dakarun RSF sun kai hare-hare akan cibiyar kiwon lafiya ta soja dake garin Um-Durman’ bayan da sojoji su ka kwace iko da yankuna masu yawa a garin da kuma makamai da albarusai a unuwar “Saliha”.

Yaki a tsakanin sojojin Sudan da kuma rundunar kai daukin gaggawa ya barke ne dai a tsakiyar watan Aprilu na 2023,wanda ya zuwa yanzu ya ci rayukan fiye da mutane 20,000 da kuma tilastawa wasu mutane miliyan 15 yin hijira, kamar yadda MDD ta bayyana.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Najeriya ta kammala dawo da alhazan da suka yi Aikin Hajjin bana

Hukumar Kula da Aikin Hajji ta Kasa (NAHCON) ta sanar da kammala dawo da dukkan  alhazan da suka yi Aikin Hajjin bana gida Najeriya daga kasar Saudiyya.

A cikin wata sanarwar da Daraktar Yaɗa Labarai ta hukumar, Fatima Sanda Usara ta fitar ranar Laraba, ta ce jirgin karshe dauke da alhazai 88 ya bar birnin Jiddah da misalin karfe 10:30 na safe dauke da alhazan jihar Kaduna da Katsina.

Kotu ta yanke hukuncin rataya ga dalibin da ya kashe malaminsa a Jos Za a fara cin tarar masu shigar banza N50,000 a Delta

A cewar hukumar, hakan ya kawo karshen jigilar da aka shafe kwana 20 ana yi tun ranar 13 ga watan Yuni.

A sakonsa na bankwana ga alhazan, shugaban NAHCON, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya bayyana godiyarsa ga Allah kan kammala aikin cikin nasara.

Ya kuma bukaci alhazan da su ci gaba da yi wa Najeriya addu’ar Allah ya kawo mata karshen tarin matsalolin da suke addabar ta.

Farfesa Abdullahi ya kuma tunatar da su cewa Aikin Hajji ibada ce da take nuna zaman lafiya da kwanciyar hankali, sannan ya buƙace su da su ci gaba da zumuncin da suka ƙulla a tsakaninsu lokacin ibadar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kungiyar Hamas Ta Sanar Da Matsayinta Kan Shirin Dakatar Da Bude Tsakaninta Da Gwamnatin Mamayar Isra’ila
  • Sheikh Na’im Kasim Yace Kare Kasa Baya Bukatar Izini Daga Wani
  • Sojojin HKI Kimani 40 Ne Suka Halaka Ko Suka Jikata A Jiya Jumma’a A Yankin Shuja’iyya Na Birnin Gaza
  • Shugaban Kasar Iran Ya Gabatar Da Jawabio A Taron Kolin Kungiyar ECO Musamman Kan Harin Da Kasarsa Ta Fuskanta
  • Kwamandan Sojojin Iran Ya Ziyarci Gidan Babban Jami’in Sojin Kasar Da Ya Yii Shahada Lokacin Yakin Baya-Bayan Nan
  • Sarayal Kuds Ta Kai Wa  Matsugunin ‘Yan Mamaya Na Sydriot Hari Da Makamai Masu Linzami
  •  Muhsin Rizai: Jagoran Juyin Musulunci Na Iran Ya Bayar Da Umarni  Da Jagorantar Yakin “Wa’adussadiq 3”
  • Mujallar “Foreign Policy”Ta Amurka: Isra’ila Ba Ta Yi Nasara A Yaki Da Iran Ba
  • NAJERIYA A YAU: Ɓoyayyun Ƙalubalen Da Sabuwar Haɗakar ADC Za Ta Iya Fuskanta
  • Najeriya ta kammala dawo da alhazan da suka yi Aikin Hajjin bana