Leadership News Hausa:
2025-08-14@14:52:19 GMT

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

Published: 15th, May 2025 GMT

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

An ce, ‘yan bindigar sun yi galaba a kan masu gadin fadar, inda suka tafi da sarkin zuwa wani wuri da ba a san ko ina ne ba.

 

Da take tabbatar da faruwar lamarin, rundunar ‘yansandan jihar Kogi ta ce, an fara gudanar da bincike, inda ta ce rundunar hadin gwiwa da ta kunshi jami’an tsaro da ‘yan banga na yankin sun fara farautar ganowa tare da kubutar da sarkin.

 

Sai dai shugaban karamar hukumar Yagba ta yamma, Hon. Tosin Olokun ya yi Allah-wadai da sace Sarkin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ruwan Wutan sojan Nijeriya Ya Kashe ‘Yan Bindiga A Zamfara.

Dakarun Operation FANSAN Yamma (OPFY) sun yi nasarar fatattakar ‘yan ta’adda da dama a wani hari da suka kai ta sama da kasa a yankin Makakkari da ke dajin Gando a karamar hukumar Bukkuyum a jihar Zamfara.

 

Wannan farmakin wanda ya gudana a ranar 10 ga watan Agustan shekarar 2025, ya biyo bayan wasu bayanan sirri da suka samu cewa dimbin ‘yan ta’addan da ke biyayya ga marigayi Halilu Buzu da Alhaji Beti sun taru a cikin dajin inda suka shirya kai harin ramuwar gayya kan al’ummomin Addabka da Nasarawan Burkullu a garin Bukkuyum.

 

Jami’in yada labarai na rundunar ‘Operation Fansan Yamma OPFY’ Kyaftin David Adewusi, ya ce bayanan sirri sun nuna cewa, harin da suka shirya kai harin shi ne ramuwar gayya da suka sha a baya-bayan nan a arangamar da suka yi da jami’an tsaro da wasu rundunonin tsaro.

 

Ya bayyana cewa, a wani samame na hadin gwiwa na kasa da ya biyo baya, dakarun da ke karkashin sashe na 2 sun kame tare da fatattakar ‘yan ta’addan da suka gudu daga inda aka kai harin ta sama.

 

Kyaftin Adewusi ya tabbatar wa ‘yan kasa masu bin doka da oda cewa ‘yan ta’adda da sauran masu rike da makamai ba za su samu mafaka a yankin Arewa maso Yamma da wasu sassan shiyyar Arewa ta tsakiya ba.

 

Ya nanata kudurin sojojin na fatattakar abokan gaba a duk inda suka taru ko kuma suka matsa sannan ya bukaci mazauna yankin da su baiwa jami’an tsaro hadin kai ta hanyar ba da rahoton abubuwa, yana mai cewa bayanan da suka dace kan lokaci na da matukar muhimmanci wajen kare al’umma da kuma kawo karshen barazanar ta’addanci da ‘yan fashi.

 

 

 

REL/AMINU DALHATU.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAF Ta Kashe ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Wata 8 A Nijeriya
  • Yadda Ƙananan Hukumomi Ke Yin Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina
  • Gwamnatin Neja Ta Tabbatar Da Kama Hatsabibin Ɗan Bindiga, Abubakar Abba
  • Ranar Hausa ta duniya: Za a yi gagarumin biki a fadar Sarkin Daura
  • An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe
  • ‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci Sun Kashe Wani Mutum Da Jikkata Wasu Da Dama A Sokoto
  • Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 
  • Ruwan Wutan sojan Nijeriya Ya Kashe ‘Yan Bindiga A Zamfara.
  • ’Yan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 6 A Taraba