Leadership News Hausa:
2025-06-19@07:47:54 GMT

Shugaba Xi Zai Kai Ziyara Kasar Rasha

Published: 4th, May 2025 GMT

Shugaba Xi Zai Kai Ziyara Kasar Rasha

Ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ta sanar da cewa, shugaban kasar Xi Jinping, zai gudanar da ziyarar aiki a kasar Rasha tsakanin ranakun 7 zuwa 10 ga watan nan na Mayu, bisa gayyatar da takwaransa na Rasha Vladimir Putin ya yi masa. Yayin wannan ziyara, shugaban na Sin zai kuma halarci bikin cika shekaru 80 da samun nasarar yakin ceton kasa na tsohuwar tarayyar Soviet, wanda zai gudana a birnin Moscow.

 

Rahotanni na cewa, yayin wannan ziyara, shugaba Xi zai gudanar da zuzzurfar tattaunawa tare da Putin, dangane da raya alakar Sin da Rasha karkashin sabon yanayin da ake ciki, da ma sauran manyan batutuwan kasa da kasa da na shiyyoyi. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka Ta Rufe Ofishin Jakadancinta Da Ke Tel-Aviv Na Haramtacciyar Kasar Isra’ila

Gwamnatin Amurka ta rufe Ofishin Jakadancinta da ke haramtacciyar kasar Isra’ila

Jakadan Amurka a haramtacciyar kasar Isra’ila Mike Huckabee ya sanar a yau Litinin cewa: Wani makami mai linzami na Iran ya fado kusa da ofishin jakadancin Amurka da ke birnin Tel Aviv, wanda ya yi barna kadan amma ba a samu rauni a tsakanin ma’aikatan ba.

A cikin wata sanarwa da ya fitar, ya ce: Daga yau Litinin ofishin jakadancin da sauran ofisoshin Amurka da suke haramtacciyar kasar Isra’ila za su ci gaba da kasancewa a rufe a matsayin matakin riga-kafi.

Jakadan ya kara da cewa: Babban abin da ya sa a gaba shi ne kare lafiyar jami’an diflomasiyyar kasarsa, kuma za su ci gaba da sanya ido kan abubuwan da ke faruwa tare da hadin gwiwar hukumomin haramtacciyar kasar Isra’ila.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya
  • Sin Za Ta Samar Da Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Gudanar Da Hada-hadar Kudin RMB Na Dijital
  • Wang Yi Ya Yi Tsokaci Kan Sakamakon Ziyarar Shugaba Xi A Kazakhstan
  • Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta
  • Tinubu Ya Kai Ziyara Benuwe Sakamakon Kisan Kiyashi Da Aka Yi Wa Jama’a
  • Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53
  • Ministan Waje: Kwakkwaran Zumunci Da Ake Sadawa Da Sin Ya Yi Tasiri Mai Kyau Ga Al’ummar Rwanda
  • Sin Ta Fatattaki Laifukan Zamba Ta Shafin Intanet 294,000 A Bara
  • Shugaba Xi Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan Kassym-Jomart Tokayev
  • Amurka Ta Rufe Ofishin Jakadancinta Da Ke Tel-Aviv Na Haramtacciyar Kasar Isra’ila