Maniyyata Daga Turai Akan Dawakai Sun Isa Kasar Saudiyya Domin Yin Aikin Hajjin 2025
Published: 4th, May 2025 GMT
Mahajjata hudu – daya daga Maroko sauran kuma daga Sifaniya – sun isa kasar Saudiyya a kan dawakai a wannan makon da ya fice don gudanar da aikin Hajjin 2025, wanda hakan ke tunatar da al’ummar Musulumi tsarin zuwa aikin hajji a shekaru da dama da suka gabata. Mahajjatan sun isa zuwa kasar Saudiyya ne ta kan iyakar Al Hadithah da ke Al Qurayyat, inda jami’an gwamnati suka tarbe su tare da duba lafiyarsu, da kuma basu abubuwan sha don jinjin irin tafiyar da suka yi ta tsawon makonni.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Kiwon Lafiya: Jihar Kwara Ta Bayyana Yadda Karancin Likitoci Ke Kawo Mata Cikas
Dakta Abdulmalik ya ce, a halin yanzu gwamnatin jihar na da likitoci 99 kadai ne, wadanda ke kan tsarin albashi, ya kara da cewa; adadin da ake bukata kuma sun kai kimanin 180 zuwa 200.
“Likitoci ukun da suka bar aiki, sun dawo bayan karin albashin likitocin da gwamnan ya yi a baya-bayan nan. Don haka, a da muna da likitoci 96, amma bayan karin albashin da gwamnan ya yi, uku da suka bar aikin sun dawo. Saboda haka, a halin yanzu muna da likitoci 99. Kazalika, muna da bukatar kari, domin kuwa kimanin likitoci 180 zuwa 200 muke bukata.”
Saboda haka, hukumar ta ce; tana kokarin samar da wata manhaja da za ta bai wa marasa lafiya, domin ziyartar cibiyoyin kiwon lafiya 45 da kuma samun bayanai kan adadin likitocin da ake da su a kowane lokaci, domin rage jinkirin da aka saba samu na ganin likita.
Ya ce, hakan kuma zai rage yanayin da marasa lafiya kan samu kansu ko kuma fita daga hayyacinsu kafin su ga likita a asibiti.
Babban Sakataren ya kara da cewa, yankunan karkara su ne wuraren da kalubalen ya fi yin kamari, ya ci gaba da cewa; hukumar na aikin samar da kudaden alawus-alawus ga likitocin, domin magance lamarin da kuma samar da kayan aiki.
“Albashin zai kasance daidai da abin da ake biya a kasashen Turai, inda yawaicin likitocin ke arcewa a matsayin balaguro”, in ji shi.
Dakta Abdulmalik ya ce, akwai wani shiri da gwamnatin jihar ke yi na kokarin cike gibin da ake da shi a bangaren likitocin jihar, inda ya ce shirin zai fara nan shekara hudu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp