An kammala Bada Horo Ga Matan Sojojin Runduna Ta 8 Da Ke Sakkwato
Published: 4th, May 2025 GMT
Babban kwamandan runduna ta 8 ta sojojin Najeriya Manjo Janar Ibikunle Ajose ya shawarci matasa a yankunan su rungumi horar da sana’o’in hannu domin inganta zamantakewa da ci gaban tattalin arziki a kasar nan.
GOC ya yi nasihar ne a wajen bikin yaye kungiyar matan jami’an rundunar soja ta 8 a cibiyar koyar da sana’o’i ta jihar Sokoto.
GOC wanda ya samu wakilcin mataimakin shugaban ma’aikata da dabaru, Kanar Raphael Olugbenga Adeyemi, GOC ya bayyana cewa, a cikin saurin ci gaban fasahar kere-kere da ci gaba da kasancewa cikin al’umma ya ta’allaka ne kan koyon sana’o’i.
Ya kara da cewa koyon fasahohin sana’o’in zai kawo ci gaba da jajircewar matasa a cikin al’umma.
A nata jawabin shugabar kungiyar Misis Meg Ndidi Ajose, uwargidan GOC ta bayyana farin cikinta tare da yabawa daliban da suka yaye bisa jajircewarsu wajen ciyar da kansu gaba.
Shugabar wadda Misis Fatima Abass ta wakilta, ta bayyana cewa cibiyar koyar da sana’o’i tana kokarin taimakawa matasa su zama masu dogaro da kai da kawo sauyi ga al’umma a yankin.
Uwargida Ajose ta yi tsokaci ne ga malamai da masu gudanar da ayyukan bisa jajircewar da suka yi wajen karfafa mata da matasa a bariki da kewaye.
Gidan rediyon Najeriya dake Sokoto ya ruwaito cewa daliban da suka kammala karatun sun samu horon ne daga sashen kere-kere da kayan abinci da hada jakunkuna da kayan kwalliya da dai sauransu.
NASIR MALALI
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Sakkwato
এছাড়াও পড়ুন:
Rabin Sojojin Isra’ila da suka ji rauni a yakin Gaza na fama da ciwon damuwa
Ma’aikatar tsaron Isra’ila ta ce fiye da sojojin kasar 20,000 ne suka ji rauni tun farkon yakin da aka fara a Gaza a watan Oktoba 2023, inda fiye da rabinsu ke fama da matsalolin lafiyar kwakwalwa, ciki har da ciwon damuwa.
A cewar sashen bayar da shawarwari na ma’aikatar, kusan kashi 56 cikin 100 na wadanda suka ji rauni sun kamu da wasu matsalolin lafiyar kwakwalwa, wanda ke nuna irin tasirin matsalar kwakwalwa da wannan rikici ke haifarwa.
Ma’aikatar ta kara da cewa kusan kashi 45 cikin 100 na wadanda suka ji rauni suna fama da raunuka a jiki, yayin da kashi 20 cikin 100 na sojojin ke fama da matsalolin kwakwalwa da na jiki a lokaci guda.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Sudan ta soki takunkuman da Amurka ta kakaba mata September 15, 2025 Dakarun Sojin Yamen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Ramon Na Isra’ila. September 14, 2025 Isra’ila Za ta Gamu Da Mummunar Martani Idan Tayi Gigin Afkawa Iran September 14, 2025 Ministocin Harkokin Wajen Kasashen Larabawa Da Na Musulmi Sun Fara Taro A Qatar. September 14, 2025 Gwamnatin Najeriya Ta Sanar Da Sabon Sharadi Na Bude Asusun Banki September 14, 2025 An Zabi Issa Tchiroma A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A Kamaru September 14, 2025 Kasar Iran Ta Yi Fatali Da Zarge-Zargen Da Kungiyar G7 Da Kawayenta Suka Yi Kanta September 14, 2025 Iran Ta Bayyana Shirinta Na Halartar Taron Shekara-Shekara Na Hukumar Makamashin Nukiliya September 14, 2025 Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Bayyana Rashin Halarta Tawagarta A Kada Kuri’a Kan Batun Falasdinu September 14, 2025 Tsananin Masifar Da Falasdinawa Ke Ciki A Gaza Saboda Hare-Haren Gwamnatin Mamayar Isra’ila September 14, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci