An kammala Bada Horo Ga Matan Sojojin Runduna Ta 8 Da Ke Sakkwato
Published: 4th, May 2025 GMT
Babban kwamandan runduna ta 8 ta sojojin Najeriya Manjo Janar Ibikunle Ajose ya shawarci matasa a yankunan su rungumi horar da sana’o’in hannu domin inganta zamantakewa da ci gaban tattalin arziki a kasar nan.
GOC ya yi nasihar ne a wajen bikin yaye kungiyar matan jami’an rundunar soja ta 8 a cibiyar koyar da sana’o’i ta jihar Sokoto.
GOC wanda ya samu wakilcin mataimakin shugaban ma’aikata da dabaru, Kanar Raphael Olugbenga Adeyemi, GOC ya bayyana cewa, a cikin saurin ci gaban fasahar kere-kere da ci gaba da kasancewa cikin al’umma ya ta’allaka ne kan koyon sana’o’i.
Ya kara da cewa koyon fasahohin sana’o’in zai kawo ci gaba da jajircewar matasa a cikin al’umma.
A nata jawabin shugabar kungiyar Misis Meg Ndidi Ajose, uwargidan GOC ta bayyana farin cikinta tare da yabawa daliban da suka yaye bisa jajircewarsu wajen ciyar da kansu gaba.
Shugabar wadda Misis Fatima Abass ta wakilta, ta bayyana cewa cibiyar koyar da sana’o’i tana kokarin taimakawa matasa su zama masu dogaro da kai da kawo sauyi ga al’umma a yankin.
Uwargida Ajose ta yi tsokaci ne ga malamai da masu gudanar da ayyukan bisa jajircewar da suka yi wajen karfafa mata da matasa a bariki da kewaye.
Gidan rediyon Najeriya dake Sokoto ya ruwaito cewa daliban da suka kammala karatun sun samu horon ne daga sashen kere-kere da kayan abinci da hada jakunkuna da kayan kwalliya da dai sauransu.
NASIR MALALI
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Sakkwato
এছাড়াও পড়ুন:
CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka
Babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na Sin CMG, ya gabatar da labarin ganawar da aka yi jiya Alhamis tsakanin shugabannin Sin da Amurka a Busan na Korea ta Kudu, cikin harsuna 85. Kuma zuwa yau Juma’a, mutanen da suka karanta rahotanni masu alaka da ganawar ta hanyoyin watsa labarai na dandalin CMG sun kai miliyan 712. Haka kuma, kafafen watsa labarai na kasa da kasa 1678, sun wallafa tare da tura rahotanni da bidiyon labaran CMG na harsuna daban daban game da ganawar, har sau 4431.
Har ila yau a wannan rana, an gudanar taron tattaunawa na kasa da kasa kan bude kofa da kirkire kirkire da ci gaba na bai daya a kasar Uruguay, wanda CMG da hadin gwiwar ofishin jakadancin Sin dake kasar suka shirya a Montevideo babban birnin Uruguay. (Mai fassara: FMM)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA