Babban kwamandan runduna ta 8 ta sojojin Najeriya Manjo Janar Ibikunle Ajose ya shawarci matasa a yankunan su rungumi horar da sana’o’in hannu domin inganta zamantakewa da ci gaban tattalin arziki a kasar nan.

 

GOC ya yi nasihar ne a wajen bikin yaye kungiyar matan jami’an rundunar soja ta 8 a cibiyar koyar da sana’o’i ta jihar Sokoto.

 

GOC wanda ya samu wakilcin mataimakin shugaban ma’aikata da dabaru, Kanar Raphael Olugbenga Adeyemi, GOC ya bayyana cewa, a cikin saurin ci gaban fasahar kere-kere da ci gaba da kasancewa cikin al’umma ya ta’allaka ne kan koyon sana’o’i.

 

Ya kara da cewa koyon fasahohin sana’o’in zai kawo ci gaba da jajircewar matasa a cikin al’umma.

 

A nata jawabin shugabar kungiyar Misis Meg Ndidi Ajose, uwargidan GOC ta bayyana farin cikinta tare da yabawa daliban da suka yaye bisa jajircewarsu wajen ciyar da kansu gaba.

 

Shugabar wadda Misis Fatima Abass ta wakilta, ta bayyana cewa cibiyar koyar da sana’o’i tana kokarin taimakawa matasa su zama masu dogaro da kai da kawo sauyi ga al’umma a yankin.

 

Uwargida Ajose ta yi tsokaci ne ga malamai da masu gudanar da ayyukan bisa jajircewar da suka yi wajen karfafa mata da matasa a bariki da kewaye.

 

Gidan rediyon Najeriya dake Sokoto ya ruwaito cewa daliban da suka kammala karatun sun samu horon ne daga sashen kere-kere da kayan abinci da hada jakunkuna da kayan kwalliya da dai sauransu.

 

NASIR MALALI

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Sakkwato

এছাড়াও পড়ুন:

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

Babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na Sin CMG, ya gabatar da labarin ganawar da aka yi jiya Alhamis tsakanin shugabannin Sin da Amurka a Busan na Korea ta Kudu, cikin harsuna 85. Kuma zuwa yau Juma’a, mutanen da suka karanta rahotanni masu alaka da ganawar ta hanyoyin watsa labarai na dandalin CMG sun kai miliyan 712. Haka kuma, kafafen watsa labarai na kasa da kasa 1678, sun wallafa tare da tura rahotanni da bidiyon labaran CMG na harsuna daban daban game da ganawar, har sau 4431.

 

Har ila yau a wannan rana, an gudanar taron tattaunawa na kasa da kasa kan bude kofa da kirkire kirkire da ci gaba na bai daya a kasar Uruguay, wanda CMG da hadin gwiwar ofishin jakadancin Sin dake kasar suka shirya a Montevideo babban birnin Uruguay. (Mai fassara: FMM)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa October 31, 2025 Daga Birnin Sin Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace October 31, 2025 Daga Birnin Sin Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda matata ta ɓace a Abuja aka tsince ta a Sakkwato
  • Sojojin Amurka Na Kara Fuskantar Venezuwela Adaidai Lokacin da Trump Ke Musanta Batun Kai Hari
  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka
  • Za mu ci gaba da shirye-shiryen babban taronmu — PDP
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi
  • Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar