Yadda Wasu Mata Ke Gallaza Wa ‘Ya’yansu Domin Bakanta Wa Mazajensu
Published: 4th, May 2025 GMT
A gaskiya wannan matsalar takan faru ne a tsakanin ma’auratan da basa son juna sosai, hadin gida (auren dangi), ko babbar matsala na karya alkawari tsakaninsu, abu ne kuma wanda bai kamata ana yi wa yara hukuncin da ba laifinsu, wannan a bayyane cin zali ne da shirin maida yaro kangarerre. Ba shi da wani amfani sai illah, dan ya kan maida yaro ya zamo baya tausayin iyayenshi, kullum yana cikin jimamin rayuwarsa a duk sanda iyayensa suka samu sabani to, a kanshi ko a kansu za a huce haushi.
Sunana Lawan Isma’il (Lisary) Jihar Kano Rano LGA:
Abin da hakan ke nufi hauka da rashin sanin yakamata. Ba shi da amfani sai rashin amfanin kansa domin na farko ta dauki alhakin yaransu, sannan kuma hakan sai dai ya kara tunzura maigidan. Babba ma kuwa domin idan uwa ta sake wannan ya zama al’adarta to ta sani watarana za ta iya rasa aurenta ko kuma ta rasa biyayya daga yaron da ake gallazawa da zarar ya gano abin da yake faruwa domin shi uban kansa zai iya dinga jawo yaron a jikinsa har sabon da yayi da mamansa ya koma kan uban. Shawarata a nan ita ce gaskiya su guji irin wannan halin da dabi’ar domin shi fa zagin iyaye ko muzgunawa yaro da iyaye suke yi baki suke wa yaro ba wai sai sun ce Allah yayi wadaran yaro ba kun ga kenan yaro tun yana karami mamansa ta jawo masa aibu tun yana karami bai ji ba bai gani ba don haka gaskiya mu iyaye muna sanin abin da za mu dinga furtawa yaranmu ko da ya ki ne ya faru tsakanin iyayensa din ba ma wani sabani ba. Allah ya kyauta ya shirya mana zurya amin.
Sunana Aminu Adamu Malam Maduri A Jihar Jigawa:
To hakika iyaye masu irin wannan dabi’a ko hali suna kuskure ne, kuma wannan kuskuren da suke zai bibiye su har karshen rayuwar su, domin dalilin wannan gallazawa da suke tana haddasa kiyayya a tsakaninsu da yaran ta har abada. Babu wani amfani domin shi fa yaro ba shi yayi laifi ba, kuma ita ma danta ne ba wai na uban ne shi kadai ba, don haka bai kamata ta musguna masa ba, saboda wai don ta rama abun da ubansa yayi mata sam-sam bai dace ba. Sosai ma kuwa, domin kuwa cigaban da yin hakan zai iya haifar da tsana a tsakanin ta da yaron kuma shi uban yaron za ta fita daga ransa wanda hakan ka’iya jawo mutuwar aure ko kuma rashin mutunta juna a zamantakewar aure. To ni dai shawara ta a nan ita ce ya kamata iyaye suna kokarin magance matsalar zaman takewar su ta aure a tsakaninsu ba tare da sa ‘ya’yansu a ciki ba, domin hakan zai taimaka wajen cigaba da zama tare da juna da samun hadin kai a tsakanin iyalai.
Sunana Hafsat Sa’eed Daga Jihar Neja:
Ni dai a nawa tunanin idan ka yi haka dan ka batawa maigidan rai ba abu ne me amfani ba kuma babu fa’ida a cikin hakan, tunda kuwa kai ka haifi danka da cikinka yadda ka ji ciwon haihuwarshi shi mijin bai ji ciwon ba, wani namijin ma babu ruwanshi dan kin gallazawa danki. Matsalar da hakan zai iya haifarwa shi ne; yaron zai ji tsanar uwar a ransa. Shawarata ya kamata duk abin da namiji zai yi miki to, ya tsaya tsakaninki da shi.
Sunana Muktari Sabo Jahun A Jihar Jigawa:
Hakika wannan tana faruwa a tsakanin ma’aurata kuma ana yin hakanne don munanawa daya barayin wanda hakan ba dai dai bane. Yin haka ba shi da wani amfani karshe ma matsala yake haifarwa a tsakanin ma’aurata ko kuma tsakanin yara da iyayensu. Tabbas hakan yana haifar da matsala domin yana kawo sabani tsakanin ma’aurata wanda har yana iya zama sanadin auren sannan kuma yana kawo kiyaiya tsakanin yara da iyayensu. Shawara a nan ita ce iyaye mata su ji tsoron Allah su daina aikata hakan domin laifin wani baya shafar wani.
Sunana Idris Haruna Zareku Miga A Jihar Jigawa:
A kan wannan batun, ana iya cewa iyaye da suke gallazawa ‘ya’yensu suna gudanar da abin kunya da rashin tausayi, wannan na iya haifar da matsaloli masu yawa ga ci gaban yara, tun daga damuwa da rashin jin dadin jiki har zuwa rashin yarda da kai. Abubuwan da zai iya zama amfaninsa za a iya ganin gallazawa a matsayin hanyar koyar da ‘ya’yansu darussa na tarbiyya da zama masu biyayya da jimrewa a cikin al’umma. Gallazawa na iya haifar da damuwa da rashin jin dadi ga ‘ya’yan, wanda zai iya shafar ingancin huldar su da iyayensu. Sannan hakan na iya haifar da rashin yarda tsakanin ‘ya’ya da iyayensu, wanda zai iya janyo rashin zaman lafiya a cikin iyali. Shawarwari ga iyaye mata da su yawaita tattaunawa tare da ‘ya’yansu, su saurari ra’ayoyinsu da jin damuwarsu, su yi kokarin gina amincewa da ‘ya’yansu ta hanyar kyakkyawar gwaninta da goyon baya, maimakon matsin lamba. Su fahimci cewa bai dace ba su rika hargitsa ‘yanu’wansu domin abubuwan da ba su ji dadin su ba, sai dai kyautata hanyar da za su koyar da su kyawawan dabi’u.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: iya haifar da da iyayensu
এছাড়াও পড়ুন:
Fizishkiyan: Wajibi Ne Musulmi Su Hada Kai Domin Dakatar Da Laifukan HKI
Shugabgan kasar Iran Mas’ud Fizishkiyan wanda ya gana da fira ministan kasar Iraqi Muahmad Shi’a Sudani a taron Doha na kasashen musulmi ya bayyana cewa; Wajibi ne kasashen musulmi su hada kai idan har suna son kawo karshen laifukan da HKI take tafkawa.
Bugu da kari, shugaban kasar ta Iran ya kuma tattaunwa wasu hanyoyin da ya kamata a yi aiki da su, matukar ana son kawo karshen ta’addancin ‘yan sahayoniya.
Shugaba Fizishkiyan ya kuma ce, laifukan da HKI take tafkawa akan fararen hula a Gaza, da kashe yara da mata ta hanyar yunwa, wani lamari ne da hankali bai iya daukarsa, kuma idan musulmi su ka hada hannu da karfe wuri daya za su kawo karshensa.
A nashi gefen Fira ministan kasar Iraki ya bayyana abinda HKI take yi da cewa, isgili ne da dokokin kasa da kasa,don haka nauyi ne da ya doru a wuyan kasashen musulmi da su yi aiki domin ganin dukar matakan da suka dace.
Haka nan kuma ya ce, taron na birnin Doha dama ce ta daukar irin wadannan matakan.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha September 15, 2025 Kwamitin Kolin Tsron Kasar Iran Ya Amince Da Yarjejeniyar Da Aka Cimma Da Hukumar IAEA September 15, 2025 Jami’in Kasar Yemen Ya Aike Da Sako Ga Mahalarta Taron Birnin Doha Na Kasar Qatar September 15, 2025 Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000 September 15, 2025 Gwamnatin Sudan Ta Ce: Babu Sulhu Da ‘Yan Tawayen Kasar Na Kungiyar Rapid Support Forces September 15, 2025 Kasashen Larabawa da na Musulmi na taron gaggawa kan harin Isra’ila a Qatar September 15, 2025 Hamas ta bukaci kasashen musulmi da na Larabawa su dauki mataki mai tsari kan Isra’ila September 15, 2025 Rabin Sojojin Isra’ila da suka ji rauni a yakin Gaza na fama da ciwon damuwa September 15, 2025 Sudan ta soki takunkuman da Amurka ta kakaba mata September 15, 2025 Dakarun Sojin Yamen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Ramon Na Isra’ila. September 14, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci