“Ka san idan za ka yi la’akari da sauran jihohin da suke barin jam’iyyarsu su shiga wata jam’iyya ni a tunanina tsoro ne karawa da babban jam’iyyar adawar da ke jihar ba, yanzu misali a Jihar Delta shi gwamnan jihar ya san daker ya ci zabe a 2023 sannan kuma yana da yakinin idan bai fita daga PDP ya shiga APC ba ba zai iya samun nasara a 2027 ba; to mu in ka yi la’akari da hakan a jam’iyyar mu ta PDP a Jihar Bauchi tun da ake mulki sau daya APC ta samu galba a 2015 sakamakon maja wanda ya ci ko’ina.

“Duk gwamnonin PDP da aka yi a Jihar Bauchi ba wanda bai kafa tarihin yin kyawawan ayyuka ba. Idan za ka kwatanta mulkin Ahmad Muazu da Dakta Malam Isa Yuguda ba za ka taba kwatantawa da abun da shi M.A Abubakar ya yi ba, kowa ya sani mulkin APC wanda M.A Abubakar ya yi ba a taba mummunar mulki irinta ba.

 

“Balle kuma yanzu da gwamna Bala Muhammad Abdulkadir ke gudanar da kyawawan ayyuka da kawo ci gaba da kyautata wa jama’a da inganta fannoni daban-daban wanda al’ummar jihar gaba daya sun yi gamsu da kokarinsa ba wani dalilin da wani zai ji sha’awar ficewa daga jam’iyyar.”

 

Ya nuna cewa duk da matsalolin da jam’iyyun siyasa ke fuskanta a Nijeriya bai takaita ga PDP zalla ba, amma ba su ji dadin yadda wasu fitattun mutane ke ficewa daga jam’iyyar ba ciki har da gwamnan jihar Delta, da tsohon gwamnan da ‘yan majalisu tarayya da na jihohi, da shugabannin kananan hukumomi a ce sun bar jam’iyyar PDP ba karamin rashi ba ne.

 

Sai dai ya tabbatar da cewa wannan matakin ba zai shafi nasarar da jam’iyyar ta saba samu a jihar Delta ba, ya tabbatar da cewa PDP ce za ta yi nasara a Delta a zaben 2027 da ke tafe.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: a jam iyyar

এছাড়াও পড়ুন:

Abin da muka sani kan labarin juyin mulki a Kwadebuwa

Kimanin kwanaki biyu ke nan ana jita-jitar cewa sojoji a sun yi nasarar hamɓarar da gwamnatin Shugaba Kasar Kwadebuwa, Alassane Ouattara.

Jita-jitar ta fara yaɗuwa ne tun bayan jin ƙarar harbe-harbe a yankunan ƙasar da dama musamman a babban birnin ƙasar na Abijan.

Ba mu tilasta wa kowa ya koma APC ba — Tinubu Jami’an tsaron Zulum sun buɗe wa Boko Haram wuta a Maiduguri

Wasu rahotanni na nuna cewa an samu ɓarkewar rikici ne a cikin birnin na Abijan, lamarin da ake hasashen ya yi sanadiyar masu zanga-zangar adawa da gwamnatin Ouattara kimanin mutum 33 cikin kwana biyu.

Sai dai har ya zuwa yanzu babu wani tabbataccen rahoton daga majiya mai ƙarfi da ke bayyana hakikanin abin da ke faruwa sakamakon ɗaukewar intanet da kuma tsayawar ayyukan gwamnati.

Har ya zuwa yanzu ba a tabbacin halin da shugaban ƙasar ke ciki, inda wasu ke zargin ya yi ɓatan dabo, wasu na ganin an kama shi inda wasu kuma na hasashen cewa ya mutu, amma dai har yanzu babu tabbas duka akai.

Har wa yau bincike ya nuna cewa wasu bidiyo da ake yadawa ake kuma danganta su da lamarin, ba na gaskiya ba ne wasu kuma ba ma daga ƙasar suka fito ba.

Ba wannan ne karo na farko da aka taɓa samun jita-jitar juyin mulki a ƙasar ba, a shekaru da dama a baya an sha samun irin wannan jita-jitar, tun bayan da wasu daga cikin ’yan ƙasar ke ganin cewa shugaban ƙasar ya zamo ɗan amshin shatan Faransa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hakar man Kolmani: Jihohin Bauchi da Gombe sun gana da NNPC kan bukatun al’umma
  • Donal Trump Ya Kori Gomomi Daga Cikin Ma’aikata A Majalisar Tsaro Ta Kasar Amurka
  • Yadda dilolin ƙwaya ke cin karensu ba babbaka a Abuja
  • Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
  • Tsokaci Kan Yadda Wasu Matasa Ke Yin Aure Ba Tare Da Sana’a Ba
  • ‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu
  • Jam’iyyar APC A Najeriya Ta Tabbatar Da Tinubu A Matsayin Dan Takarar Shugaban Kasa A Jam’iyyar A Shekara Ta 2027
  • SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (2)
  • Allah Ya Isa: Shugaban PDP Damagun ya musanta zargin yi wa APC aiki
  • Abin da muka sani kan labarin juyin mulki a Kwadebuwa