Babu Dalilin Da Zai Sanya Wasu Mambobin PDP Ficewa A Jam’iyyar A Bauchi
Published: 3rd, May 2025 GMT
“Ka san idan za ka yi la’akari da sauran jihohin da suke barin jam’iyyarsu su shiga wata jam’iyya ni a tunanina tsoro ne karawa da babban jam’iyyar adawar da ke jihar ba, yanzu misali a Jihar Delta shi gwamnan jihar ya san daker ya ci zabe a 2023 sannan kuma yana da yakinin idan bai fita daga PDP ya shiga APC ba ba zai iya samun nasara a 2027 ba; to mu in ka yi la’akari da hakan a jam’iyyar mu ta PDP a Jihar Bauchi tun da ake mulki sau daya APC ta samu galba a 2015 sakamakon maja wanda ya ci ko’ina.
“Balle kuma yanzu da gwamna Bala Muhammad Abdulkadir ke gudanar da kyawawan ayyuka da kawo ci gaba da kyautata wa jama’a da inganta fannoni daban-daban wanda al’ummar jihar gaba daya sun yi gamsu da kokarinsa ba wani dalilin da wani zai ji sha’awar ficewa daga jam’iyyar.”
Ya nuna cewa duk da matsalolin da jam’iyyun siyasa ke fuskanta a Nijeriya bai takaita ga PDP zalla ba, amma ba su ji dadin yadda wasu fitattun mutane ke ficewa daga jam’iyyar ba ciki har da gwamnan jihar Delta, da tsohon gwamnan da ‘yan majalisu tarayya da na jihohi, da shugabannin kananan hukumomi a ce sun bar jam’iyyar PDP ba karamin rashi ba ne.
Sai dai ya tabbatar da cewa wannan matakin ba zai shafi nasarar da jam’iyyar ta saba samu a jihar Delta ba, ya tabbatar da cewa PDP ce za ta yi nasara a Delta a zaben 2027 da ke tafe.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: a jam iyyar
এছাড়াও পড়ুন:
Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba
Wannan ya janyo tambayoyi kan ko za ta iya komawa nan take.
A lokacin da aka tambaye ta me take yi a lokacin da aka dakatar da ita, Sanata Natasha ta ce ba ta tsaya ba, har yanzu tana gudanar da ayyuka tare da wakiltar mutanenta.
“Na kasance ina aiki a duk lokacin. Na ci gaba da aiki kuma ina shirin gabatar da wasu dokoki a kan ma’adanai. Ba zan iya miƙa su ga wani ba,” in ji ta.
Ta ƙara da cewa duk da cewa ba ta halartar zaman majalisa, ta ci gaba da yin ayyukan ci gaba ga mutanenta.
“Fitar da ni daga majalisa ba kawai ni aka daƙile ba, an hana muryar Kogi ta Tsakiya fitowa fili,” in ji ta.
“Majalisar Dattawa ta hana mata da yara ‘yan Nijeriya samjn wakilci. Yanzu muna da Sanata mata guda uku kacal, alhali a baya muna da takwas.”
LEADERSHIP ta ruwaito cewa sanarwar dawowarta da aka shirya yi a ranar Talata ta tayar da hankula a majalisar, inda aka tsaurara tsaro kuma aka kawo motocin jami’an tsaro da dama.
Shige da fice daga harabar majalisar ya kasance a ƙarƙashin kulawar jami’an tsaro, inda ake bincikar motoci kafin ba su iznin shiga.
Ko da yake ba ta koma majalisar ba tukuna, Sanata Natasha ta jaddada cewa za ta ci gaba da yin aikinta.
“Ina da niyyar ci gaba da wakiltar Kogi ta Tsakiya da Nijeriya gaba ɗaya,” in ji ta.
“Ko na je majalisa ko ban je ba, zan ci gaba da sauke nauyin da ke kaina.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp