Kotu Ta Daure Wasu Mutum Biyu Da Suka Yi Wa Yarinya ‘Yar Shekara 14 Fyade A Birnin Kebbi
Published: 3rd, May 2025 GMT
Wadanda ake tuhumar dai sun tabbatar wa kansu aikata laifin ba tare da kara yin wata shaida ba.
Duk da haka, a kokarin janye ikirari nasu, sun yarda cewa abokai ne kuma suna zaune tare a wurin da suka aikata laifin, kuma aka kama su tare.
Tawagar masu gabatar da kara karkashin jagorancin Barista Zainab M.
Lauyan wanda ake kara ya kalubalanci nauyin da ke tattare da ikirarin wadanda ake kara suka gabatar a gaban kotu wajen tabbatar da laifukan da ake tuhumarsu da su.
Sai dai bayan dukkan bangarorin biyu sun amince da rubutaccen adireshinsu na karshe, kotun ta yanke hukuncin.
Kotun ta yanke wa wadanda ake tuhumar hukuncin zaman gidan kaso a kan laifin hada baki na aikata fyade. Idan aka yi la’akari da laifin hada baki na cin zarafi, an umurci wadanda ake tuhumar da su biya tarar Naira Dubu Dari biyu da Hamsin (N250,000) ko kuma zaman gidan yari na shekara daya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: wadanda ake
এছাড়াও পড়ুন:
Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara
Yarjejeniyar, a cewar daukacin mahalarta taron, ta nuna wani gagarumin mataki na kawo karshen tashe-tashen hankula, garkuwa da mutane da satar shanu a Arewa maso Yamma, da kuma yankin Arewa.
Yarjejeniyar wacce Mai Maradin Katsina da Hakimin Kurfi, Alhaji Mansur Amadu Kurfi, da shugaban karamar hukumar, Babangida Abdullahi Kurfi suka shirya, ta gudana ne a dajin Wurma, inda ake fama da rashin tsaro.
Manyan jagororin ‘yan bindigan da suka hada da Alhaji Usman Kachalla Ruga da Sani Muhindinge da Yahaya Sani (Hayyu) da kuma Alhaji Shu’aibu duk sun yi alkawarin tsagaita wuta.
Daga baya suka sako mutanen da suka kama kuma suka bar manoma su koma gonakansu ba tare da wata barazana ba.
Sai dai kasa da wata guda da kulla yarjejeniyar, an tattaro cewa ‘yan bindigar sun sake kai hari a Zamfara inda suka yi awon gaba da masallata da dama.
Wata majiya ta cikin garin, ta shaida cewa, harin ya afku ne a lokacin sallar asuba da misalin karfe 5:30 na safe, inda ‘yan bindigar suka afkawa masallacin, suka kewaye shi, sannan suka tattara masallatan zuwa daji.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp